< Isaiah 27 >

1 At that time the Lord will take his sharp, large, and strong sword, and punish Leviathan, the slithering serpent, and Leviathan, the coiled serpent, and he will kill the sea dragon.
A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
2 At that time, sing about a beautiful vineyard.
A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
3 I, the Lord, take care of it, watering it often. I guard it night and day so that nobody can damage it.
Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
4 I'm not angry anymore. If there are thorns and brambles I would go and fight them, burning them all up,
Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
5 Otherwise they should come to me for protection. They should make their peace with me, yes, make their peace with me.
Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
6 In the future the descendants of Jacob will be like a tree taking root. Israel will flower and send out shoots, and fill the whole world with fruit!
A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
7 Has the Lord hit Israel as he hit those that attacked them? Were they killed like their killers were killed?
Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
8 You dealt with them by sending them into exile, by banishing them. He drove them away with his powerful force, like when the east wind blows.
Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
9 Through this experience Jacob's guilt will be forgiven. The removal of their sins will come to fruition when they take all the pagan altar stones and crush them to pieces like chalk—no Asherah poles or altars of incense will be left standing.
A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
10 The fortified city will be abandoned, its houses as empty and lonely as a desert. Cattle will graze and rest there, stripping bare the branches of its trees.
Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
11 Their dry branches are broken off and used by women to make fires. This is a people that doesn't have any sense, so their Maker won't feel sorry for them, and their Creator won't help them.
Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
12 At that time the Lord will thresh the grain harvested from the Euphrates River to the Wadi of Egypt, and you Israelites will be gathered up one by one.
A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
13 At that time a loud trumpet will sound, and those who were dying in Assyria will return along with those exiled in Egypt. They will come and worship the Lord on the holy mountain in Jerusalem.
Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.

< Isaiah 27 >