< Genesis 45 >

1 Joseph couldn't control his emotions any longer while all his attendants were there, so he shouted out, “Everybody leave me!” So there was nobody else there when Joseph revealed who he was to his brothers.
Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
2 But he cried so loudly that the Egyptians could hear him, and they told Pharaoh's household about it.
Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
3 “I'm Joseph!” he announced to his brothers. “Is my father still alive?” They couldn't answer him as they were so surprised to see him face to face.
Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
4 “Please come closer to me,” he told his brothers. They came over to him. “I'm your brother Joseph who you sold into slavery in Egypt.
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
5 But don't be worried or get angry with yourselves that you sold me to be a slave here, because it was God who sent me ahead of you to save lives.
Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
6 The country has suffered from famine for two years already, but there will be five more years with no plowing or reaping.
Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
7 God sent me ahead of you to make sure you would still have descendants, to save your lives in this miraculous way.
Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
8 So it wasn't you who sent me here, but God. He was the one who made me Pharaoh's chief advisor in charge of all his affairs, and ruler of the whole country of Egypt.
“Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
9 Now hurry! Go back to my father and tell him, ‘This message comes from your son Joseph: God has made me the ruler of the whole of Egypt. Come to me now; don't wait.
Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
10 You'll live in the land of Goshen so you can be close to me with your children and grandchildren, and with your flocks and herds and everything that belongs to you.
Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
11 I'll make sure you have food, because there are still five more years of famine to come. Otherwise you and your family and your animals are going to starve.’”
Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
12 Then Joseph told his brothers, “You can all see for yourselves—including my brother Benjamin—that it's really me talking to you!
“Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
13 Tell my father how much I'm respected in Egypt. Tell him everything that you've seen. Hurry! Bring my father here quickly!”
Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
14 He hugged Benjamin, and Benjamin hugged him back. They both wept for joy.
Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
15 He kissed all his brothers and wept over them, and after that his brothers were able to start talking with him.
Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
16 Word soon reached Pharaoh's palace that Joseph's brothers had arrived. Pharaoh and his officials were glad to hear the news.
Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
17 Pharaoh said to Joseph, “Tell your brothers, ‘This is what you are to do: Load your donkeys with grain and go back to the country of Canaan.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
18 Then bring your father and your families and return here to me. I will give you the best land in Egypt, and you shall eat the best food the country has to offer.’
Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
19 Tell them to do this as well, ‘Take some wagons from Egypt for your children and your wives. Bring them and your father here.
“An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
20 Don't worry about bringing your possessions because the best of all Egypt is yours.’”
Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
21 So that's what the sons of Israel did. Joseph provided them with wagons, as Pharaoh had ordered. He also gave them supplies for their journey.
Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
22 He gave each of them new clothes. But to Benjamin he gave five sets of clothes and 300 pieces of silver.
Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
23 Joseph also sent to his father the following: ten donkeys carrying the best things from Egypt, and ten female donkeys carrying grain and bread and supplies needed for his father's journey.
Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
24 Then he saw his brothers off, and as they left he told them, “Don't argue on the way!”
Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
25 So they left Egypt and went back home to their father Jacob in the country of Canaan.
Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
26 “Joseph's still alive!” they told him. “It's true, and he's the ruler of the whole country of Egypt!” Jacob was stunned at the news—he just couldn't believe it!
Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
27 But when they told him everything that Joseph had said to them, and when he saw the wagons that Joseph had sent to take him to Egypt, Jacob came back to his senses.
Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
28 Israel said, “All right, I believe you! My son Joseph is still alive! I'm going to go and see him before I die.”
Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”

< Genesis 45 >