< Genesis 10 >

1 The following are the genealogies of the sons of Noah: Shem, Ham, and Japheth. They had sons born to them after the flood.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 The sons of Japheth: Gomer, Magog, Madai, Javan, Tubal, Meshech, and Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 The sons of Gomer: Ashkenaz, Riphath, and Togarmah.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 The sons of Javan: Elishah, Tarshish, Kittim, and Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 The descendants of these ancestors spread throughout the coastal areas, each group having their own language, with their families developing into different nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 The sons of Ham: Cush, Mizraim, Put, and Canaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 The sons of Cush: Seba, Havilah, Sabtah, Raamah, and Sabteca. The sons of Raamah: Sheba and Dedan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Cush was also the father of Nimrod, who set himself up as the first tyrant on earth.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 He was a powerful fighter who defied the Lord; which is why there's the expression, “Like Nimrod, a powerful fighter who defied the Lord.”
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 His kingdom began in the cities of Babel, Erech, Akkad, and Calneh, all located in the land of Shinar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 From there he moved into Assyria and built the cities of Nineveh, Rehoboth-Ir, Calah,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 and Resen, which lies between Nineveh and the great city of Calah.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 Mizraim was the father of the Ludites, the Anamites, the Lehabites, the Naphtuhites,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 the Pathrusites, the Casluhites, and the Caphtorites (ancestors of the Philistines).
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Canaan was the father of Sidon, his firstborn, and of the Hittites,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 the Jebusites, the Amorites, the Girgashites,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 the Hivites, the Arkites, the Sinites,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 the Arvadites, the Zemarites, and the Hamathites. Later the Canaanite tribes spread out
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 and the territory of the Canaanites stretched from Sidon towards Gerar and all the way to Gaza, then towards Sodom, Gomorrah, Admah, and Zeboiim, all the way to Lasha.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 These were the sons of Ham according to their tribes, languages, lands, and nation.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 Shem, whose older brother was Japheth, also had sons. Shem was the forefather of all the sons of Eber.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 The sons of Shem: Elam, Asshur, Arphaxad, Lud, and Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 The sons of Aram: Uz, Hul, Gether, and Mash.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Arphaxad was the father of Shelah. Shelah was the father of Eber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 Eber had two sons. One was named Peleg, because in his time the earth was divided; the name of his brother was Joktan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Joktan was the father of Almodad, Sheleph, Hazarmaveth, Jerah,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 Hadoram, Uzal, Diklah,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 Obal, Abimael, Sheba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 Ophir, Havilah, and Jobab. These were all sons of Joktan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 They lived in the land lying between Mesha to Sephar, in the hill country to the east.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 These were the sons of Shem, according to their tribes, languages, lands, and nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 These were all the tribes descended from Noah's sons, according to their genealogies and national groups. From these ancestors the different nations of the earth spread around the world after the flood.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.

< Genesis 10 >