< Amos 7 >

1 This is what the Lord God showed me. I saw that he was preparing a swarm of locusts just when the spring crops began to grow. (Spring crops begin to grow right after the time when the king's hay is cut.)
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
2 And so when the locusts finished eating every green plant in the fields, I pleaded with the Lord God, “Please forgive your people! How can the descendants of Jacob survive? They are so weak.”
Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
3 So the Lord changed his mind. “It won't happen,” said the Lord.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
4 This is what the Lord God showed me. I saw that the Lord God was calling for a judgment of fire. The fire burned up the depths of the sea and destroyed the farmland.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
5 I pleaded with the Lord God, “Please stop! How can the descendants of Jacob survive? They are so weak.”
Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
6 So the Lord changed his mind. “This too won't happen,” said the Lord.
Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
7 This is what he showed me. I saw the Lord was standing beside a wall that had been built with a plumb line. He was holding a plumb line in his hand.
Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
8 And the Lord asked me, “Amos, what do you see?” I replied, “A plumb line.” And the Lord God said, “I am placing a plumb line in the midst of my people Israel. I won't ignore their sins anymore.
Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
9 The high places of the descendents of Isaac will be torn down, and the holy places of Israel will be destroyed. Sword in hand, I will rise up against the house of Jeroboam.”
“Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
10 Then Amaziah, priest of Bethel, sent a message to Jeroboam, king of Israel, saying, “Amos is plotting against you among the people of Israel. What he's saying is unbearable!
Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
11 For he's saying Jeroboam will be killed by the sword, and the people will be taken away from their land into exile.”
Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
12 Amaziah said to Amos, “Go away prophet! Run away to the land of Judah. Go and prophesy there to earn your bread.
Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
13 But don't ever prophesy again at Bethel, for this is where the king worships, the national Temple.”
Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
14 But Amos replied, “I'm not a trained prophet, or the son of a prophet. I was just a shepherd, and also took care of fig trees.
Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
15 The Lord took me from following my flock, and the Lord told me, ‘Go, and give my message to my people of Israel.’”
Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
16 So now hear what the Lord is telling you: You say, “Don't prophesy against Israel, and don't preach against the descendants of Isaac.”
Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
17 But this is what the Lord says: Your wife will become a prostitute in the city; your sons and daughters will be killed by the sword. Your land will be measured and divided up, and you yourself will die in a foreign land. The people of Israel will definitely be taken from the land and go into exile.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”

< Amos 7 >