< 2 Samuel 9 >

1 David said, “Is there anyone still left of Saul's family so I can be kind to him for Jonathan's sake?”
Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
2 There was a man called Ziba who used to be a servant of Saul's family. They called for him to come to David, and the king asked him, “Are you Ziba?” “Yes, I am your servant,” he replied.
To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
3 The king asked him, “Is there anyone still left of Saul's family so I can be kind to him as I promised before God?” “There's still one of Jonathan's sons, who is lame in both feet,” Ziba replied.
Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
4 “Where is he?” asked the king. “He's in the town of Lo-debar, living in the home of Machir, son of Ammiel,” Ziba replied.
Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
5 So King David had him brought from Machir's home.
Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
6 When Mephibosheth, son of Jonathan, son of Saul, came to David, he bowed facedown to the ground in respect. Then David said, “Welcome Mephibosheth.” “I am your servant,” he replied.
Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
7 “Do not be afraid,” said David, “for I will truly be kind to you for the sake of your father Jonathan. I will return to you all the land owned by your grandfather Saul, and you will always eat at my table.”
Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
8 Mephibosheth bowed down and said, “Who am I, your servant, that you should pay any attention to a dead dog like me?”
Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
9 Then the king called for Saul's servant Ziba and told him, “I have given to your master's grandson everything that belonged to Saul and his family.
Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
10 You and your sons and workers are to farm the ground for him and bring in the produce, so that your master's grandson will have food to eat. But Mephibosheth, your master's grandson, will always eat at my table.” Ziba had fifteen sons and twenty workers.
Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
11 Ziba replied to the king, “My lord the king, your servant will do everything that you have commanded.” So Mephibosheth ate at David's table like one of the king's sons.
Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
12 Mephibosheth had a young son named Mica. All the people who lived in Ziba's house became Mephibosheth's servants.
Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
13 But Mephibosheth lived in Jerusalem, because he always ate at the king's table. He was lame in both feet.
Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.

< 2 Samuel 9 >