< 2 Kings 13 >

1 Jehoahaz, son of Jehu, became king of Israel in the twenty-third year of the reign of Joash, son of Ahaziah, king of Judah. He reigned in Samaria for seventeen years.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 He did what was evil in the Lord's sight, and followed the sins that Jeroboam son of Nebat, had made Israel commit; he did not end them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 So the Lord was angry with Israel, and he repeatedly allowed them to be defeated by Hazael, king of Aram, and his son Ben-hadad.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Jehoahaz asked the Lord for help, and the Lord responded to his request because he saw how badly the king of Aram was treating Israel.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 The Lord gave Israel someone who would save them so they no longer were under Aramean rule. Then the Israelites were able to go back to living in safety as before.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Even so they did not end the sins that the house of Jeroboam had made Israel commit—they continued to follow them. The Asherah idol still stood in Samaria.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 All that was left of Jehoahaz's army were fifty horsemen, ten chariots, and ten thousand soldiers, for the king of Aram had destroyed the rest, turning them into dust like that when grain is threshed.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 The rest of what happened in Jehoahaz's reign, all he did, and his great achievements are recorded in the Book of Chronicles of the Kings of Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 Jehoahaz died and was buried in Samaria. His son Jehoash succeeded him as king.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 Jehoash, son of Jehoahaz, became king of Israel in Samaria in the thirty-seventh year of the reign of King Joash of Judah, and he reigned for sixteen years.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 He did what was evil in the Lord's sight and did not end all the sins that Jeroboam, son of Nebat, had made Israel commit—he continued to follow them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 The rest of what happened in Jehoash's reign, all he did, and his great achievements such as his war against Amaziah, king of Judah, are recorded in the Book of Chronicles of the Kings of Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 Jehoash died, and Jeroboam sat on his throne. Jehoash was buried in Samaria with the kings of Israel.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Elisha had become ill with a disease that would eventually kill him. Jehoash, king of Israel, went to visit him, and wept over him, saying, “My father, my father, the chariots and the horsemen of Israel!”
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Elisha told him, “Find a bow and some arrows.” So Jehoash found a bow and some arrows.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Then Elisha said to the king of Israel, “Pick up the bow.” So the king picked up the bow. Elisha placed his hands on the king's hands.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 “Open the east window,” he told him. So the king opened it and Elisha said, “Shoot!” So he fired an arrow. Then Elisha explained, “This is the Lord's victory arrow representing the arrow of victory over the Arameans. You will attack the Arameans in Aphek and finish them off.”
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Then Elisha said, “Pick up the arrows!” So he picked them up. Elisha told the king of Israel, “Hit the ground with them!” He hit the ground three times, and then stopped.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 The man of God got angry with him, telling him, “You should have hit the ground five or six times. Then you would have attacked the Arameans until you had completely destroyed them. But now you will only attack the Arameans three times.”
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Elisha died and was buried. Raiders from the country of Moab used to invade Israel every spring.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 On time some Israelites were burying a man when suddenly they saw some raiders coming, so they quickly threw the man into Elisha's tomb. As soon as he touched Elisha's bones, the man came back to life and stood up.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Hazael, king of Aram, caused problems for Israel through all Jehoahaz's reign.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 But the Lord graciously helped them and was kind to them. He looked after them because of his agreement with Abraham, Isaac, and Jacob. Even to this day he's been unwilling to destroy them or to throw them out of his presence.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 When Hazael, king of Aram, died, his son Ben-hadad succeeded him as king.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 Then Jehoash, son of Jehoahaz, recovered from Ben-hadad son of Hazael, the towns that Hazael had captured from his father Jehoahaz. Jehoash defeated Ben-hadad three times, and so recaptured the Israelite towns.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kings 13 >