< Luke 8 >

1 Now it happened after this that He started going around town by town, village by village, preaching and proclaiming the good news of the Kingdom of God, and the twelve were with Him;
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 also certain women who had been healed of malignant spirits and infirmities: Mary (the one called Magdalene) from whom seven demons had gone out;
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 and Joanna the wife of Chuza, an official of Herod; and Susanna, and many others—these were providing for Him from their substance.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Now when a large crowd had gathered, with people coming to Him from town after town, He spoke by a parable:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 “A sower went out to sow his seed; and as he sowed some fell along the road, and it got trampled, and the birds of the air devoured it.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 And some fell on the rock ledge, and upon sprouting it withered, because it had no moisture.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 And some fell among thorns, and springing up together the thorns choked it.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 The rest fell into the good ground, and growing up it produced fruit a hundredfold.” Upon saying these things He called out, “He who has ears to hear, let him hear!”
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Then His disciples asked Him saying, “What does this parable mean?”
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 So He said: “To you it has been given to know the mysteries of the Kingdom of God, but to the rest only in parables, so that ‘seeing they may not see, and hearing they may not understand.’
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 “Now here is the parable: The seed is the Word of God.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 Those along the road are those who hear; then the devil comes and takes away the word from their hearts, in order that they not be saved, having believed.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Those on the rock ledge are the ones who, whenever they hear, receive the word with joy; yet these have no root, who believe for a while and in time of testing fall away.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Now that which fell into the thorns: these are the ones who heard, yet as they go they are choked by cares, riches, and pleasures of life, and bring no fruit to maturity.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 But that on the good ground: these are the ones who having heard the word with a noble and good heart, hold on to it and produce fruit with perseverance.”
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Upon saying these things He called out: “He who has ears to hear, let him hear! No one, when he has lit a lamp, covers it with a vessel or puts it under a bed, but he sets it on a lamp stand, so that those who come in may see the light.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Further, there is nothing hidden that will not be revealed, nor anything concealed that will not be made known and come into the open.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 So be careful how you hear: Because whoever has, to him more will be given; and whoever does not have, even what he thinks he has will be taken away from him.”
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Then His mother and brothers came to Him, and they could not get near Him because of the crowd.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 And it was told Him by some saying, “Your mother and your brothers are standing outside, wanting to see you.”
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 But in answer He said to them, “My mother and my brothers are these, the ones who hear the word of God and do it!”
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Now it happened on one of those days that He got into a boat with His disciples; and He said to them, “Let us go over to the other side of the lake.” So they launched out.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 But as they sailed He fell asleep. A windstorm descended on the lake, and they were being swamped and were in jeopardy.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 So they came and awakened Him, saying, “Master, Master, we are perishing!” Then He got up and rebuked the wind and the waves of water—and they stopped, and there was a calm!
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 So He said to them, “Where is your faith?” But being terrified they marveled, saying to each other: “Who can this be? Because He commands even the winds and the water, and they obey Him!”
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Then they sailed to the district of the Gadarenes, which is opposite Galilee.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Well when He stepped out on the land, a certain man of that town met Him, who had had demons for a long time—he wore no clothes, nor did he live in a house, but among the tombs.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 When he saw Jesus he gave a yell, fell down before Him, and with a loud voice he said: “What do you want with me, Jesus, Son of the Most High God? I beg you, don't torment me!”
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 because He had commanded the unclean spirit to get out of the man (it had seized him many times—he would be bound with chains and shackles, being kept under guard; then bursting the bonds he would be driven by the demon into deserted places).
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Then Jesus asked him, “What is your name?” And he said, “Legion” (because many demons had gone into him).
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 And he kept imploring Him that He would not order them to go away into the Abyss. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Now a herd of many pigs was feeding there on the hillside; and they started begging Him that He would allow them to go into those; so He gave them permission.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Then the demons exited the man and entered the pigs—and the herd rushed down the steep bank into the lake and was drowned!
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Well when the herders saw what had happened they ran away and reported it in the town and in the countryside.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 So they went out to see what had happened, and came to Jesus; they found the man from whom the demons had gone out sitting at Jesus' feet, clothed and in his right mind; and they were afraid.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Also, the eyewitnesses reported to them how the demonized man was healed.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Then the whole multitude from the surrounding region of the Gadarenes asked Him to depart from them, because they were overcome by fear. So He got into the boat and returned.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Now the man from whom the demons had gone out had started begging Him that he might be with Him. But Jesus sent him away, saying,
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 “Return to your house and recount how much God has done for you.” So he went his way and proclaimed all over town how much Jesus had done for him.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Now it happened, when Jesus returned, that the crowd welcomed Him, because they were all waiting for Him.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 And then, there came a man named Jairus, and he was a ruler of the synagogue; he fell down at Jesus' feet and started begging Him to come to his house,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 because he had an only daughter, about twelve years old, and she was dying. Now as He was going, the crowds were pressing against Him.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 And a woman—suffering with a flow of blood for twelve years, who had spent her whole livelihood on physicians, but could not be healed by any—
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 approaching from behind touched the border of His garment; and immediately the flow of her blood stopped!
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 So Jesus said, “Who touched me?” When all denied it, Peter and those with him said: “Master, the people are pressing against you and crowding in, and you say, ‘Who touched me?’”
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 But Jesus said, “Someone did touch me, because I noticed power going out from me.”
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Now when the woman saw that she could not hide, she came trembling, and falling down before Him she told Him in the presence of all the people the reason why she had touched Him, and how she was healed immediately.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 So He said: “Courage, daughter, your faith has healed you. Go into peace.”
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 While He was still speaking, here came someone from the synagogue ruler's house, saying to him: “Your daughter has died. Don't bother the teacher.”
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 But upon hearing it Jesus reacted by saying to him, “Don't be afraid; just believe and she will be healed.”
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 When He arrived at the house, He allowed no one to go in except Peter, John, James, the father of the child, and her mother.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Now all were weeping and mourning for her; but He said, “Do not weep; she is not dead, but sleeping.”
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 They started ridiculing Him, knowing that she had died.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 So He put them all outside, and grasping her hand He called, saying, “Child, arise!”
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Then her spirit returned, and she got right up! And He directed that she be given something to eat.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Her parents were astonished, but He charged them to tell no one what had happened.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >