< Luke 17 >

1 Then He said to the disciples: “Things that cause people to fall are bound to come, but woe to him through whom they do come!
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 It would be better for him if a millstone were hung around his neck and he were thrown into the sea, than that he should cause one of these little ones to fall.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Watch out for yourselves: if your brother sins against you, rebuke him; and if he repents, forgive him.
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 Even if he sins against you seven times in a day, and seven times in that day returns, saying, ‘I repent,’ you must forgive him.”
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 The apostles said to the Lord, “Increase our faith.”
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 So the Lord said: “If you had faith like a mustard seed has, you could say to this mulberry tree, ‘Be uprooted, and be planted in the sea,’ and it would obey you.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 “And which of you, having a slave plowing or tending sheep, will say to him when he comes in from the field, ‘Come at once and recline to eat’?
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 Will he not rather say to him, ‘Prepare something for me to eat, and gird yourself and serve me until I eat and drink, and afterward you will eat and drink’?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 Does he thank that slave because he did the things commanded? I guess not!
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 So likewise you, whenever you have done everything you were told to do, say, ‘We are unworthy slaves, because we have only done what we were supposed to.’”
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 Now as He was traveling toward Jerusalem, He went along between Samaria and Galilee.
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 And as He entered a certain village, ten men met Him—being lepers they stood at a distance.
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 They called out, saying, “Jesus, Master, have mercy on us!”
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 And paying attention He said to them, “Go and show yourselves to the priests.” It happened that as they went they were cleansed!
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 Well one of them, when he saw that he was healed, returned, glorifying God with a loud voice;
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 then he fell on his face at His feet, thanking Him—and he was a Samaritan!
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 So Jesus reacted by saying: “Were not all ten cleansed? So where are the nine?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 None were found to return and give glory to God except this foreigner!”
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 Then He said to him, “Get up and go; your faith has made you well.”
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Now when He was asked by the Pharisees when the Kingdom of God would come, He answered them and said: “The Kingdom of God does not come with observation;
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 nor will they say, ‘Look, here!’ or ‘Look, there!’ because indeed the Kingdom of God is within you.”
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 Then He said to the disciples: “Days are coming when you will long to see one of the days of the Son of the Man, and you will not see it.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 And they will say to you, ‘Look, here!’ or ‘Look, there!’ Do not go along or follow.
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 Because just like the lightning that lights the whole sky when it flashes, so also will the Son of the Man be in His day.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 But first He must suffer many things and be rejected by this generation.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 Also, just as it was in the days of Noah, so will it also be in the days of the Son of the Man.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 They were eating, drinking, marrying and being given in marriage, until the day that Noah entered the ark, and the flood came and destroyed them all.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 Likewise also as it was in the days of Lot; they were eating, drinking, buying, selling, planting, building—
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 but on the day Lot went out from Sodom, fire and brimstone rained down from heaven and destroyed them all.
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 Even so will it be in the day when the Son of the Man is revealed.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 “In that day, he who is on the housetop, and his goods in the house, let him not go down to get them; and likewise he who is in the field, let him not turn back.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Remember Lot's wife!
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Whoever seeks to save his life will lose it, and whoever ‘wastes’ it will preserve it.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 I tell you: on that night there will be two men in one bed; one will be taken and the other left.
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 Two women will be grinding together; one will be taken and the other left.”
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 They reacted by saying to Him, “Where, Lord?” He said to them, “Where there is a carcass, there will the vultures also be gathered.”
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< Luke 17 >