< Psalms 17 >

1 The prayer of David. Hear, O Lord, my justice: attend to my supplication. Give ear unto my prayer, which proceedeth not from deceitful lips.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Let my judgment come forth from thy countenance: let thy eyes behold the things that are equitable.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Thou hast proved my heart, and visited it by night, thou hast tried me by fire: and iniquity hath not been found in me.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 That my mouth may not speak the works of men: for the sake of the words of thy lips, I have kept hard ways.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Perfect thou my goings in thy paths: that my footsteps be not moved.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 I have cried to thee, for thou, O God, hast heard me: O incline thy ear unto me, and hear my words.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Shew forth thy wonderful mercies; thou who savest them that trust in thee.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 From them that resist thy right hand keep me, as the apple of thy eye. Protect me under the shadow of thy wings.
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 From the face of the wicked who have afflicted me. My enemies have surrounded my soul:
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 They have shut up their fat: their mouth hath spoken proudly.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 They have cast me forth and now they have surrounded me: they have set their eyes bowing down to the earth.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 They have taken me, as a lion prepared for the prey; and as a young lion dwelling in secret places.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Arise, O Lord, disappoint him and supplant him; deliver my soul from the wicked one: thy sword
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 From the enemies of thy hand. O Lord, divide them from the few of the earth in their life: their belly is filled from thy hidden stores. They are full of children: and they have left to their little ones the rest of their substance.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 But as for me, I will appear before thy sight in justice: I shall be satisfied when thy glory shall appear.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalms 17 >