< Proverbs 6 >

1 My son, if thou be surety for thy friend, thou hast engaged fast thy hand to a stranger.
Ɗana, in ka shirya tsaya wa maƙwabcinka don yă karɓi bashi, in ka sa hannunka don ɗaukar lamunin wani,
2 Thou art ensnared with the words of thy mouth, and caught with thy own words.
in maganarka ta taɓa kama ka, ko kalmomin bakinka sun zama maka tarko,
3 Do therefore, my son, what I say, and deliver thyself: because thou art fallen into the hand of thy neighbour. Run about, make haste, stir up thy friend:
to, sai ka yi haka, ɗana don ka’yantar da kanka; da yake ka shiga hannuwan maƙwabcinka, ka tafi ka ƙasƙantar da kanka; ka roƙi maƙwabcinka!
4 Give not sleep to thy eyes, neither let thy eyelids slumber.
Ka hana kanka barci, ko gyangyaɗi a idanunka ma.
5 Deliver thyself as a doe from the hand, and as a bird from the hand of the fowler.
Ka’yantar da kanka, kamar barewa daga hannun mai farauta, kamar tsuntsu daga tarkon mai kafa tarko.
6 Go to the ant, O sluggard, and consider her ways, and learn wisdom:
Ku tafi wurin kyashi, ku ragwaye; ku lura da hanyoyinsa ku zama masu hikima!
7 Which, although she hath no guide, nor master, nor captain,
Ba shi da jagora ba shugaba ko mai mulki,
8 Provideth her meat for herself in the summer, and gathereth her food in the harvest.
duk da haka yakan yi tanade-tanadensa da rani ya kuma tattara abincinsa a lokacin girbi.
9 How long wilt thou sleep, O sluggard? when wilt thou rise out of thy sleep?
Har yaushe za ku kwanta a can, ku ragwaye? Yaushe za ku farka daga barcinku?
10 Thou wilt sleep a little, thou wilt slumber a little, thou wilt fold thy hands a little to sleep:
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
11 And want shall come upon thee, as a traveller, and poverty as a man armed. But if thou be diligent, thy harvest shall come as a fountain, and want shall flee far from thee.
talauci kuwa zai zo kamar’yan hari rashi kuma kamar ɗan fashi.
12 A man that is an apostate, an unprofitable man, walketh with a perverse mouth,
Sakare da mutumin banza wanda yana yawo da magana banza a baki,
13 He winketh with the eyes, presseth with the foot, speaketh with the finger.
wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
14 With a wicked heart he deviseth evil, and at all times he soweth discord.
wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
15 To such a one his destruction shall presently come, and he shall suddenly be destroyed, and shall no longer have any remedy.
Saboda haka masifa za tă fāɗa farat ɗaya; za a hallaka shi nan da nan, ba makawa.
16 Six things there are, which the Lord hateth, and the seventh his soul detesteth:
Akwai abubuwa shida da Ubangiji ya ƙi, abubuwa bakwai da suke abin ƙyama gare shi,
17 Haughty eyes, a lying tongue, hands that shed innocent blood,
duban reni, harshe mai ƙarya, hannuwa masu zub da jinin marar laifi,
18 A heart that deviseth wicked plots, feet that are swift to run into mischief,
zuciyar da take ƙulla mugayen dabaru, ƙafafun da suke sauri zuwa aikata mugunta,
19 A deceitful witness that uttereth lies, and him that soweth discord among brethren.
mai shaidar ƙarya wanda yake zuba ƙarairayi, da kuma mutumin da yake tā-da-na-zaune-tsaye a cikin’yan’uwa.
20 My son, beep the commandments of thy father, and forsake not the law of thy mother.
Ɗana, ka kiyaye umarnan mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
21 Bind them in thy heart continually, and put them about thy neck.
Ka ɗaura su a zuciyarka har abada; ka ɗaura su kewaye da wuyanka.
22 When thou walkest, let them go with thee: when thou sleepest, let them keep thee; and when thou awakest, talk with them.
Sa’ad da kake tafiya, za su bishe ka; sa’ad da kake barci, za su lura da kai; sa’ad da ka farka, za su yi maka magana.
23 Because the commandment is a lamp, and the law a light, and reproofs of instruction are the way of life:
Gama waɗannan umarnai fitila ne, wannan koyarwa haske ne, kuma gyare-gyaren horo hanyar rayuwa ce,
24 That they may keep thee from the evil woman, and from the flattering tongue of the stranger.
suna kiyaye ka daga mace marar ɗa’a daga sulɓin harshen mace marar aminci.
25 Let not thy heart covet her beauty, be not caught with her winks:
Kada ka yi sha’awarta a cikin zuciyarka kada ka bar ta tă ɗauki hankalinka da idanunta.
26 For the price of a harlot is scarce one loaf: but the woman catcheth the precious soul of a man.
Gama karuwa takan mai da kai kamar burodin kyauta, mazinaciya kuma takan farauci ranka.
27 Can a man hide fire in his bosom, and his garments not burn?
Mutum zai iya ɗiba wuta ya zuba a cinyarsa ba tare da rigunansa sun ƙone ba?
28 Or can he walk upon hot coals, and his feet not be burnt?
Mutum zai iya yin tafi a garwashi wuta mai zafi ba tare da ƙafafunsa sun ƙone ba?
29 So he that goeth in to his neighbour’s wife, shall not be clean when he shall touch her.
Haka yake da wanda ya kwana da matar wani; babu wanda ya taɓa ta da zai tafi babu hukunci.
30 The fault is not so great when a man hath stolen: for he stealeth to fill his hungry soul:
Mutane ba sa ƙyale ɓarawo in ya yi sata don yă ƙosar da yunwarsa sa’ad da yake jin yunwa.
31 And if he be taken he shall restore sevenfold, and shall give up all the substance of his house.
Duk da haka in aka kama shi, dole yă biya sau bakwai ko da yake abin zai ci dukan arzikin gidansa.
32 But he that is an adulterer, for the folly of his heart shall destroy his own soul:
Amma mutumin da ya yi zina ba shi da hankali; duk wanda ya yi haka yana hallaka kansa ne.
33 He gathereth to himself shame and dishonour, and his reproach shall not be blotted out:
Dūka da kunya ne za su zama rabonsa, kuma kunyarsa za tă dawwama.
34 Because the jealousy and rage of the husband will not spare in the day of revenge,
Gama kishi kan tā da hasalar miji, kuma ba zai ji tausayi ba sa’ad da yake ramawa.
35 Nor will he yield to any man’s prayers, nor will he accept for satisfaction ever so many gifts.
Ba zai karɓi duk wata biya ba; zai ƙi cin hanci, kome yawansu.

< Proverbs 6 >