< Numbers 1 >

1 And the Lord spoke to Moses in the desert of Sinai in the tabernacle of the covenant, the first day of the second month, the second year of their going out of Egypt, saying:
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Take the sum of all the congregation of the children of Israel by their families, and houses, and the names of every one, as many as are of the male sex,
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 From twenty years old and upwards, of all the men of Israel fit for war, and you shall number them by their troops, thou and Aaron.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 And there shall be with you the princes of the tribes, and of the houses in their kindreds,
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 Whose names are these: Of Ruben, Elisur the son of Sedeur.
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 Of Simeon, Salamiel the son of Surisaddai.
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 Of Juda, Nahasson the son of Aminadab.
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Of Issachar, Nathanael the son of Suar.
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 Of Zabulon, Eliab the son of Helon.
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 And of the sons of Joseph: of Ephraim, Elisama the son of Ammiud: of Manasses, Gamaliel the son of Phadassur.
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 Of Benjamin, Abidan the son of Gedeon.
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 Of Dan, Ahiezer the son of Ammisaddai.
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 Of Aser, Phegiel the son of Ochran.
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 Of Gad, Eliasaph the son of Duel.
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Of Nephtali, Ahira the son of Enan.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 These are the most noble princes of the multitude by their tribes and kindreds, and the chiefs of the army of Israel:
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 Whom Moses and Aaron took with all the multitude of the common people:
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 And assembled them on the first day of the second month, reckoning them up by the kindreds, and houses, and families, and heads, and names of every one from twenty years old and upward,
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 As the Lord had commanded Moses. And they were numbered in the desert of Sinai.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 Of Ruben the eldest son of Israel, by their generations and families and houses and names of every head, all that were of the male sex, from twenty years old and upward, that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 Were forty-six thousand five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Of the sons of Simeon by their generations and families, and houses of their kindreds, were reckoned up by the names and heads of every one, all that were of the male sex, from twenty years old and upward, that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 Fifty-nine thousand three hundred.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Of the sons of Gad, by their generations and families and houses of their kindreds were reckoned up by the names of every one from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 Forty-five thousand six hundred and fifty.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Of the sons of Juda, by their generations and families and houses of their kindreds, by the names of every one from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 Were reckoned up seventy-four thousand six hundred.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Of the sons of Issachar, by their generations and families and houses of their kindreds, by the names of every one from twenty years old and upward, all that could go forth to war,
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 Were reckoned up fifty-four thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Of the sons of Zabulon, by the generations and families and houses of their kindreds, were reckoned up by the names of every one from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 Fifty-seven thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Of the sons of Joseph, namely, of the sons of Ephraim, by the generations and families and houses of their kindreds, were reckoned up by the names of every one, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 Forty thousand five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Moreover of the sons of Manasses, by the generations and families and houses of their kindreds, were reckoned up by the names of every one from twenty years old and upward, all that could go forth to war,
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 Thirty-two thousand two hundred.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Of the sons of Benjamin, by their generations and families and houses of their kindreds, were reckoned up by the names of every one from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 Thirty-five thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Of the sons of Dan, by their generations and families and houses of their kindreds, were reckoned up by the names of every one from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 Sixty-two thousand seven hundred.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Of the sons of Aser, by their generations and families and houses of their kindreds, were reckoned up by the names of every one from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 Forty-one thousand and five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 Of the sons of Nephtali, by their generations and families and houses of their kindreds, were reckoned up by the names of every one from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war,
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 Fifty-three thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 These era they who were numbered by Moses and Aaron, and the twelve princes of Israel, every one by the houses of their kindreds.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 And the whole number of the children of Israel by their houses and families, from twenty years old and upward, that were able to go to war,
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 Were six hundred and three thousand five hundred and fifty men.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 But the Levites in the tribes of their families were not numbered with them.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 Number not the tribe of Levi, neither shalt thou put down the sum of them with the children of Israel:
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 But appoint them over the tabernacle of the testimony, and all the vessels thereof, and whatsoever pertaineth to the ceremonies. They shall carry the tabernacle and all the furniture thereof: and they shall minister, and shall encamp round about the tabernacle.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 When you are to go forward, the Levites shall take down the tabernacle: when you are to camp, they shall set it up. What stranger soever cometh to it, shall be slain.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 And the children of Israel shall camp every man by his troops and bands and army.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 But the Levites shall pitch their tents round about the tabernacle, lest there come indignation upon the multitude of the children of Israel, and they shall keep watch, and guard the tabernacle of the testimony.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 And the children of Israel did according to all things which the Lord had commanded Moses.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 1 >