< Nehemiah 1 >

1 The words of Nehemias the son of Helchias. And it came to pass in the month of Casleu, in the twentieth year, as I was in the castle of Susa,
Kalmomin Nehemiya ɗan Hakaliya. A cikin watan Kisleb a shekara ta ashirin, yayinda nake a fadar Shusha.
2 That Hanani one of my brethren came, he and some men of Juda; and I asked them concerning the Jews, that remained and were left of the captivity, and concerning Jerusalem.
Hanani, ɗaya daga cikin’yan’uwana, ya zo daga Yahuda tare da waɗansu mutane. Na kuwa tambaye shi game da raguwar Yahudawan da suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta, da kuma game da Urushalima.
3 And they said to me: They that have remained, and are left of the captivity there in the province, are in great affliction, and reproach: and the wall of Jerusalem is broken down, and the gates thereof are burnt with fire.
Suka ce mini, “Waɗanda suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta da kuma suka komo cikin yankin suna cikin babban damuwa da wulaƙanci. An rushe katangar Urushalima aka kuma ƙone ƙofofin da wuta.”
4 And when I had heard these words, I sat down, and wept, and mourned for many days: and I fasted, and prayed before the face of the God of heaven.
Da na ji waɗannan abubuwa, sai na zauna na yi kuka. Na yi kwanaki ina makoki da azumi, na kuma yi addu’a a gaban Allah na sama.
5 And I said: I beseech thee, O Lord God of heaven, strong, great, and terrible, who keepest covenant and mercy with those that love thee, and keep thy commandments:
Na ce, “Ya Ubangiji Allah na sama, Allah mai girma da mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna da waɗanda suke ƙaunarsa, suke kuma yin biyayya da umarnansa,
6 Let thy ears be attentive, and thy eyes open, to hear the prayer of thy servant, which I pray before thee now, night and day, for the children of Israel thy servants: and I confess the sins of the children of Israel, by which they have sinned against thee: I and my father’s house have sinned.
ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
7 We have been seduced by vanity, and have not kept thy commandments, and ceremonies and judgments, which thou hast commanded thy servant Moses.
Mun yi mugunta gare ka. Ba mu yi biyayya da umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da ka ba wa bawanka Musa ba.
8 Remember the word that thou commandedst to Moses thy servant, saying: If you shall transgress, I will scatter you abroad among the nations:
“Ka tuna da umarnan da ka ba wa bawanka Musa, kana cewa, ‘In kun yi rashin aminci, zan warwatsar da ku a cikin al’ummai,
9 But if you return to me, and keep my commandments, and do them, though you should be led away to the uttermost parts of the world, I will gather you from thence, and bring you back to the place which I have chosen for my name to dwell there.
amma in kuka dawo gare ni kuka kuma yi biyayya da umarnaina, to, ko mutanenku da aka kwasa zuwa zaman bauta suna can wuri mafi nisa, zan tattara su daga can in kawo su wurin da na zaɓa yă zama wurin zama don Sunana.’
10 And these are thy servants, and thy people: whom thou hast redeemed by thy great strength, and by thy mighty hand.
“Su bayinka ne da kuma mutanenka da ka fansa ta wurin ƙarfinka mai girma da kuma hannunka mai iko.
11 I beseech thee, O Lord, let thy ear be attentive to the prayer of thy servant, and to the prayer of thy servants who desire to fear thy name: and direct thy servant this day, and give him mercy before this man. For I was the king’s cupbearer.
Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.

< Nehemiah 1 >