< Luke 17 >

1 And he said to his disciples: It is impossible that scandals should not come: but woe to him through whom they come.
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 It were better for him, that a millstone were hanged about his neck, and he cast into the sea, than that he should scandalize one of these little ones.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Take heed to yourselves. If thy brother sin against thee, reprove him: and if he do penance, forgive him.
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 And if he sin against thee seven times in a day, and seven times in a day be converted unto thee, saying, I repent; forgive him.
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 And the apostles said to the Lord: Increase our faith.
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 And the Lord said: If you had faith like to a grain of mustard seed, you might say to this mulberry tree, Be thou rooted up, and be thou transplanted into the sea: and it would obey you.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 But which of you having a servant ploughing, or feeding cattle, will say to him, when he is come from the field: Immediately go, sit down to meat:
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 And will not rather say to him: Make ready my supper, and gird thyself, and serve me, whilst I eat and drink, and afterwards thou shalt eat and drink?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 Doth he thank that servant, for doing the things which he commanded him?
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 I think not. So you also, when you shall have done all these things that are commanded you, say: We are unprofitable servants; we have done that which we ought to do.
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 And it came to pass, as he was going to Jerusalem, he passed through the midst of Samaria and Galilee.
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 And as he entered into a certain town, there met him ten men that were lepers, who stood afar off;
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 And lifted up their voice, saying: Jesus, master, have mercy on us.
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 Whom when he saw, he said: Go, shew yourselves to the priests. And it came to pass, as they went, they were made clean.
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 And one of them, when he saw that he was made clean, went back, with a loud voice glorifying God.
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 And he fell on his face before his feet, giving thanks: and this was a Samaritan.
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 And Jesus answering, said, Were not ten made clean? and where are the nine?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 There is no one found to return and give glory to God, but this stranger.
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 And he said to him: Arise, go thy way; for thy faith hath made thee whole.
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 And being asked by the Pharisees, when the kingdom of God should come? he answered them, and said: The kingdom of God cometh not with observation:
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 Neither shall they say: Behold here, or behold there. For lo, the kingdom of God is within you.
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 And he said to his disciples: The days will come, when you shall desire to see one day of the Son of man; and you shall not see it.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 And they will say to you: See here, and see there. Go ye not after, nor follow them:
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 For as the lightening that lighteneth from under heaven, shineth unto the parts that are under heaven, so shall the Son of man be in his day.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 But first he must suffer many things, and be rejected by this generation.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 And as it came to pass in the days of Noe, so shall it be also in the days of the Son of man.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 They did eat and drink, they married wives, and were given in marriage, until the day that Noe entered into the ark: and the flood came and destroyed them all.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 Likewise as it came to pass, in the days of Lot: they did eat and drink, they bought and sold, they planted and built.
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 And in the day that Lot went out of Sodom, it rained fire and brimstone from heaven, and destroyed them all.
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 Even thus shall it be in the day when the Son of man shall be revealed.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 In that hour, he that shall be on the housetop, and his goods in the house, let him not go down to take them away: and he that shall be in the field, in like manner, let him not return back.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Remember Lot’s wife.
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Whosoever shall seek to save his life, shall lose it: and whosoever shall lose it, shall preserve it.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 I say to you: in that night there shall be two men in one bed; the one shall be taken, and the other shall be left.
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 Two women shall be grinding together: the one shall be taken, and the other shall be left: two men shall be in the field; the one shall be taken, and the other shall be keft.
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
36 They answering, say to him: Where, Lord?
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 Who said to them: Wheresoever the body shall be, thither will the eagles also be gathered together.
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< Luke 17 >