< Psalms 34 >

1 [A Psalm] of David; when he changed his behaviour before Abimelech, who drove him away, and he departed. I will bless Jehovah at all times; his praise shall continually be in my mouth.
Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
2 My soul shall make its boast in Jehovah: the meek shall hear, and rejoice.
Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
3 Magnify Jehovah with me, and let us exalt his name together.
Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
4 I sought Jehovah, and he answered me, and delivered me from all my fears.
Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
5 They looked unto him, and were enlightened, and their faces were not confounded.
Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
6 This afflicted one called, and Jehovah heard [him], and saved him out of all his troubles.
Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
7 The angel of Jehovah encampeth round about them that fear him, and delivereth them.
Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
8 Taste and see that Jehovah is good: blessed is the man that trusteth in him!
Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
9 Fear Jehovah, ye his saints; for there is no want to them that fear him.
Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
10 The young lions are in need and suffer hunger; but they that seek Jehovah shall not want any good.
Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
11 Come, ye sons, hearken unto me: I will teach you the fear of Jehovah.
Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
12 What man is he that desireth life, [and] loveth days, that he may see good?
Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
13 Keep thy tongue from evil, and thy lips from speaking guile;
ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
14 Depart from evil, and do good; seek peace, and pursue it.
Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
15 The eyes of Jehovah are upon the righteous, and his ears are toward their cry;
Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
16 The face of Jehovah is against them that do evil, to cut off the remembrance of them from the earth:
fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
17 [The righteous] cry, and Jehovah heareth, and delivereth them out of all their troubles.
Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
18 Jehovah is nigh to those that are of a broken heart, and saveth them that are of a contrite spirit.
Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
19 Many are the adversities of the righteous, but Jehovah delivereth him out of them all:
Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
20 He keepeth all his bones; not one of them is broken.
yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
21 Evil shall destroy the wicked; and they that hate the righteous shall bear their guilt.
Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
22 Jehovah redeemeth the soul of his servants; and none of them that trust in him shall bear guilt.
Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.

< Psalms 34 >