< Matthew 22 >

1 And Jesus answering spoke to them again in parables, saying,
Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
2 The kingdom of the heavens has become like a king who made a wedding feast for his son,
“Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
3 and sent his bondmen to call the persons invited to the wedding feast, and they would not come.
Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
4 Again he sent other bondmen, saying, Say to the persons invited, Behold, I have prepared my dinner; my oxen and my fatted beasts are killed, and all things ready; come to the wedding feast.
Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
5 But they made light of it, and went, one to his own land, and another to his commerce.
Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
6 And the rest, laying hold of his bondmen, ill-treated and slew [them].
Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
7 And [when] the king [heard of it he] was wroth, and having sent his forces, destroyed those murderers and burned their city.
Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
8 Then he says to his bondmen, The wedding feast is ready, but those invited were not worthy;
Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
9 go therefore into the thoroughfares of the highways, and as many as ye shall find invite to the wedding feast.
Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
10 And those bondmen went out into the highways, and brought together all as many as they found, both evil and good; and the wedding feast was furnished with guests.
Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
11 And the king, having gone in to see the guests, beheld there a man not clothed with a wedding garment.
Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
12 And he says to him, [My] friend, how camest thou in here not having on a wedding garment? But he was speechless.
Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
13 Then said the king to the servants, Bind him feet and hands, and take him away, and cast him out into the outer darkness: there shall be the weeping and the gnashing of teeth.
Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
14 For many are called ones, but few chosen ones.
Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
15 Then went the Pharisees and held a council how they might ensnare him in speaking.
Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
16 And they send out to him their disciples with the Herodians, saying, Teacher, we know that thou art true and teachest the way of God in truth, and carest not for any one, for thou regardest not men's person;
Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
17 tell us therefore what thou thinkest: Is it lawful to give tribute to Caesar, or not?
To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
18 But Jesus, knowing their wickedness, said, Why tempt ye me, hypocrites?
Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
19 Shew me the money of the tribute. And they presented to him a denarius.
Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
20 And he says to them, Whose [is] this image and superscription?
Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
21 They say to him, Caesar's. Then he says to them, Pay then what is Caesar's to Caesar, and what is God's to God.
Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
22 And when they heard [him], they wondered, and left him, and went away.
Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
23 On that day came to him Sadducees, who say there is no resurrection; and they demanded of him,
A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
24 saying, Teacher, Moses said, If any one die, not having children, his brother shall marry his wife and shall raise up seed to his brother.
cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
25 Now there were with us seven brethren; and the first having married died, and not having seed, left his wife to his brother.
Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
26 In like manner also the second and the third, unto the seven.
Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
27 And last of all the woman also died.
Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
28 In the resurrection therefore of which of the seven shall she be wife, for all had her?
To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
29 And Jesus answering said to them, Ye err, not knowing the scriptures nor the power of God.
Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
30 For in the resurrection they neither marry nor are given in marriage, but are as angels of God in heaven.
Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
31 But concerning the resurrection of the dead, have ye not read what was spoken to you by God, saying,
Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
32 I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob? God is not God of [the] dead, but of [the] living.
'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
33 And when the crowds heard [it] they were astonished at his doctrine.
Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
34 But the Pharisees, having heard that he had put the Sadducees to silence, were gathered together.
Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
35 And one of them, a lawyer, demanded, tempting him, and saying,
Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
36 Teacher, which is the great commandment in the law?
“Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
37 And he said to him, Thou shalt love [the] Lord thy God with all thy heart, and with all thy soul, and with all thy understanding.
Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
38 This is [the] great and first commandment.
Wannan itace babbar doka ta farko.
39 And [the] second is like it, Thou shalt love thy neighbour as thyself.
Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
40 On these two commandments the whole law and the prophets hang.
Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
41 And the Pharisees being gathered together, Jesus demanded of them,
Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
42 saying, What think ye concerning the Christ? whose son is he? They say to him, David's.
Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
43 He says to them, How then does David in Spirit call him Lord, saying,
Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
44 The Lord said to my Lord, Sit on my right hand until I put thine enemies under thy feet?
“Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
45 If therefore David call him Lord, how is he his son?
Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
46 And no one was able to answer him a word, nor did any one dare from that day to question him any more.
Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.

< Matthew 22 >