< 2 Chronicles 21 >

1 And Jehoshaphat slept with his fathers, and was buried with his fathers in the city of David; and Jehoram his son reigned in his stead.
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 And he had brethren, the sons of Jehoshaphat: Azariah and Jehiel, and Zechariah, and Azariah, and Michael, and Shephatiah: all these were sons of Jehoshaphat king of Israel.
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
3 And their father had given them great gifts of silver and of gold and of precious things, besides fortified cities in Judah; but the kingdom he gave to Jehoram, for he was the firstborn.
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
4 And Jehoram established himself over the kingdom of his father, and strengthened himself; and he slew all his brethren with the sword, and [certain] also of the princes of Israel.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
5 Jehoram was thirty-two years old when he began to reign; and he reigned eight years in Jerusalem.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
6 And he walked in the way of the kings of Israel, as did the house of Ahab, for the daughter of Ahab was his wife; and he did evil in the sight of Jehovah.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
7 But Jehovah would not destroy the house of David, because of the covenant that he had made with David, and as he had promised to give to him always a lamp, and to his sons.
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
8 In his days Edom revolted from under the hand of Judah, and they set a king over themselves.
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
9 And Jehoram went over with his captains, and all the chariots with him; and he rose up by night, and smote the Edomites who had surrounded him, and the captains of the chariots.
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
10 But the Edomites revolted from under the hand of Judah unto this day. Then Libnah revolted at the same time from under his hand, because he had forsaken Jehovah the God of his fathers.
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
11 Moreover he made high places on the mountains of Judah, and caused the inhabitants of Jerusalem to commit fornication, and compelled Judah [thereto].
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
12 And there came a writing to him from Elijah the prophet saying, Thus saith Jehovah, the God of David thy father: Because thou hast not walked in the ways of Jehoshaphat thy father, nor in the ways of Asa king of Judah,
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
13 but hast walked in the way of the kings of Israel, and hast made Judah and the inhabitants of Jerusalem to commit fornication, like the fornications of the house of Ahab, and also hast slain thy brethren, thy father's house who were better than thyself:
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
14 behold, Jehovah will smite with a great stroke thy people, and thy children, and thy wives, and all thy substance,
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
15 and thyself with sore sicknesses, with a disease of thy bowels, until thy bowels fall out by reason of the sickness day by day.
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
16 And Jehovah stirred up against Jehoram the spirit of the Philistines, and of the Arabians, who [are] near the Ethiopians;
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
17 and they came up into Judah, and broke into it, and carried away all the substance that was found in the king's house, and his sons also, and his wives; so that there was no son left him, except Jehoahaz the youngest of his sons.
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
18 And after all this, Jehovah smote him in his bowels with an incurable sickness.
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
19 And it came to pass, from day to day, and at the time when the second year was drawing to a close, that his bowels fell out by reason of his sickness, and he died in cruel sufferings. And his people made no burning for him, like the burning of his fathers.
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
20 He was thirty-two years old when he began to reign, and he reigned in Jerusalem eight years, and departed without being regretted. And they buried him in the city of David, but not in the sepulchres of the kings.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.

< 2 Chronicles 21 >