< 1 Thessalonians 5 >

1 But concerning the times and the seasons, brethren, ye have no need that ye should be written to,
To,’yan’uwa, game da lokuta da ranaku, ba ma bukata mu rubuta muku,
2 for ye know perfectly well yourselves, that the day of [the] Lord so comes as a thief by night.
gama kun sani sarai cewa ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo da dare.
3 When they may say, Peace and safety, then sudden destruction comes upon them, as travail upon her that is with child; and they shall in no wise escape.
Yayinda mutane suke cewa, “Akwai salama da zaman lafiya,” hallaka za tă auko musu farat ɗaya, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba za su kuwa tsira ba.
4 But ye, brethren, are not in darkness, that the day should overtake you as a thief:
Amma ku,’yan’uwa, ba kwa cikin duhu da wannan rana za tă zo muku ba zato kamar ɓarawo.
5 for all ye are sons of light and sons of day; we are not of night nor of darkness.
Dukanku’ya’yan haske ne da kuma’ya’yan rana. Mu ba mutanen dare ko na duhu ba ne.
6 So then do not let us sleep as the rest do, but let us watch and be sober;
Saboda haka fa, kada mu zama kamar saura, waɗanda suke barci, sai dai mu zama masu tsaro da masu kamunkai.
7 for they that sleep sleep by night, and they that drink drink by night;
Gama masu barci, da dad dare suke barci, masu sha su bugu kuwa, da dad dare suke buguwa.
8 but we being of [the] day, let us be sober, putting on [the] breastplate of faith and love, and as helmet [the] hope of salvation;
Amma da yake mu na rana ne, bari mu zama masu kamunkai, sanye da bangaskiya da ƙauna kamar sulke, begen cetonmu kuma kamar hular kwano.
9 because God has not set us for wrath, but for obtaining salvation through our Lord Jesus Christ,
Gama Allah bai naɗa mu don mu sha fushi ba, sai dai mu sami ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
10 who has died for us, that whether we may be watching or sleep, we may live together with him.
Ya mutu saboda mu domin, ko muna a faɗake ko muna barci, mu kasance tare da shi.
11 Wherefore encourage one another, and build up each one the other, even as also ye do.
Saboda haka ku ƙarfafa juna ku kuma gina juna, kamar dai yadda kuke yi.
12 But we beg you, brethren, to know those who labour among you, and take the lead among you in [the] Lord, and admonish you,
To, muna roƙonku,’yan’uwa, ku girmama waɗanda suke aiki sosai a cikinku, waɗanda suke bisanku cikin Ubangiji da kuma waɗanda suke yin muku gargaɗi.
13 and to regard them exceedingly in love on account of their work. Be in peace among yourselves.
Ku riƙe su da mutunci sosai cikin ƙauna saboda aikinsu. Ku yi zaman lafiya da juna.
14 But we exhort you, brethren, admonish the disorderly, comfort the faint-hearted, sustain the weak, be patient towards all.
Muna kuma gargaɗe ku,’yan’uwa, ku gargaɗe waɗanda suke zaman banza, ku ƙarfafa masu raunanar zuciya, ku taimaki marasa ƙarfi, ku yi haƙuri da kowa.
15 See that no one render to any evil for evil, but pursue always what is good towards one another and towards all;
Ku tabbata cewa kada kowa yă rama mugunta da mugunta, sai dai kullum ku yi ƙoƙarin yin wa juna alheri da kuma dukan mutane.
16 rejoice always;
Ku riƙa farin ciki kullum;
17 pray unceasingly;
ku ci gaba da yin addu’a;
18 in everything give thanks, for this is [the] will of God in Christ Jesus towards you;
ku yi godiya cikin kowane hali, gama wannan shi ne nufin Allah dominku cikin Kiristi Yesu.
19 quench not the Spirit;
Kada ku danne aikin Ruhu.
20 do not lightly esteem prophecies;
Kada ku rena annabci,
21 but prove all things, hold fast the right;
amma ku gwada kome, ku riƙe abin da yake mai kyau,
22 hold aloof from every form of wickedness.
ku ƙi kowace mugunta.
23 Now the God of peace himself sanctify you wholly: and your whole spirit, and soul, and body be preserved blameless at the coming of our Lord Jesus Christ.
Bari Allah da kansa, Allah na salama, yă tsarkake ku sarai. Bari dukan ruhunku, ranku, da kuma jikinku su zama marar aibi a dawowar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
24 He [is] faithful who calls you, who will also perform [it].
Wannan wanda ya kira ku mai aminci ne zai kuwa aikata.
25 Brethren, pray for us.
’Yan’uwa, ku yi mana addu’a.
26 Greet all the brethren with a holy kiss.
Ku gaggai da dukan’yan’uwa da sumba mai tsarki.
27 I adjure you by the Lord that the letter be read to all the [holy] brethren.
Na gama ku da Ubangiji ku sa a karanta wannan wasiƙa ga dukan’yan’uwa.
28 The grace of our Lord Jesus Christ [be] with you.
Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku.

< 1 Thessalonians 5 >