< 1 Samuel 8 >

1 And it came to pass when Samuel was old, that he made his sons judges over Israel.
Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
2 And the name of his firstborn was Joel; and the name of his second, Abijah; they judged in Beer-sheba.
Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
3 And his sons walked not in his ways, but turned aside after lucre, and took bribes, and perverted justice.
Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
4 Then all the elders of Israel gathered themselves together, and came to Samuel to Ramah,
Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
5 and said to him, Behold, thou art become old, and thy sons walk not in thy ways: now appoint us a king to judge us, like all the nations.
Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
6 And the thing displeased Samuel, when they said, Give us a king to judge us. And Samuel prayed to Jehovah.
Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
7 And Jehovah said to Samuel, Hearken unto the voice of the people in all that they say unto thee: for they have not rejected thee, but they have rejected me, that I should not reign over them.
Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
8 According to all the deeds that they have done since the day that I brought them up out of Egypt even unto this day, in that they have forsaken me and served other gods, so do they also unto thee.
Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
9 And now hearken unto their voice; only, testify solemnly unto them, and declare unto them the manner of the king that shall reign over them.
Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
10 And Samuel spoke all the words of Jehovah to the people that asked of him a king.
Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
11 And he said, This will be the manner of the king that shall reign over you: he will take your sons, and appoint them for himself, on his chariot and among his horsemen, and they shall run before his chariots;
Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
12 and [he will take them] that he may appoint for himself captains over thousands, and captains over fifties, and that they may plough his ground, and reap his harvest, and make his instruments of war and instruments of his chariots.
Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
13 And he will take your daughters for perfumers, and cooks, and bakers.
Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
14 And your fields, and your vineyards, and your oliveyards, the best, will he take and give to his servants.
Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
15 And he will take the tenth of your seed and of your vineyards, and give to his chamberlains and to his servants.
Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
16 And he will take your bondmen, and your bondwomen, and your comeliest young men, and your asses, and use them for his work.
Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
17 He will take the tenth of your sheep. And ye shall be his servants.
Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
18 And ye shall cry out in that day because of your king whom ye have chosen; and Jehovah will not answer you in that day.
Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
19 And the people refused to hearken to the voice of Samuel; and they said, No, but there shall be a king over us,
Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
20 that we also may be like all the nations; and our king shall judge us, and go out before us, and conduct our wars.
Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
21 And Samuel heard all the words of the people, and he repeated them in the ears of Jehovah.
Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
22 And Jehovah said to Samuel, Hearken unto their voice, and make them a king. And Samuel said to the men of Israel, Go ye every man to his city.
Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”

< 1 Samuel 8 >