< 1 Kings 11 >

1 But king Solomon loved many foreign women, besides the daughter of Pharaoh: women of the Moabites, Ammonites, Edomites, Zidonians, Hittites;
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 of the nations of which Jehovah had said to the children of Israel, Ye shall not go in to them, neither shall they come in to you; they would certainly turn away your heart after their gods: to these Solomon was attached in love.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 And he had seven hundred wives, princesses, and three hundred concubines; and his wives turned away his heart.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 And it came to pass when Solomon was old, [that] his wives turned away his heart after other gods; and his heart was not perfect with Jehovah his God, as the heart of David his father.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 And Solomon went after Ashtoreth the goddess of the Zidonians, and after Milcom the abomination of the Ammonites.
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 And Solomon did evil in the sight of Jehovah, and followed not fully Jehovah, as David his father.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 Then did Solomon build a high place for Chemosh the abomination of the Moabites, on the hill that is before Jerusalem, and for Molech the abomination of the children of Ammon.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 And so he did for all his foreign wives, who burned incense and sacrificed to their gods.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 And Jehovah was angry with Solomon, because his heart was turned away from Jehovah the God of Israel, who had appeared to him twice,
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 and had commanded him concerning this thing, not to go after other gods; but he kept not what Jehovah had commanded.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 And Jehovah said to Solomon, Forasmuch as this is done by thee, and thou hast not kept my covenant and my statutes which I commanded thee, I will certainly rend the kingdom from thee, and will give it to thy servant:
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 notwithstanding in thy days I will not do it, for David thy father's sake; I will rend it out of the hand of thy son;
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 only, I will not rend away all the kingdom: I will give one tribe to thy son, for David my servant's sake, and for Jerusalem's sake which I have chosen.
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 And Jehovah stirred up an adversary to Solomon, Hadad the Edomite; he was of the king's seed in Edom.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 Now it came to pass when David was in Edom, when Joab the captain of the host had gone up to bury the slain, after he had smitten every male in Edom
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 (for Joab abode there six months with all Israel, until he had cut off every male in Edom),
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 that Hadad fled, he and certain Edomites of his father's servants with him, to go into Egypt, Hadad being yet a little child.
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 And they arose out of Midian, and came to Paran, and took men with them out of Paran, and they came to Egypt, to Pharaoh king of Egypt; who gave him a house, and appointed him victuals, and gave him land.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 And Hadad found great favour in the sight of Pharaoh, and he gave him as wife the sister of his own wife, the sister of Tahpenes the queen.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 And the sister of Tahpenes bore him Genubath his son; and Tahpenes brought him up in Pharaoh's house; and Genubath was in Pharaoh's household, among the sons of Pharaoh.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 And Hadad heard in Egypt that David slept with his fathers, and that Joab the captain of the host was dead; and Hadad said to Pharaoh, Let me depart, that I may go to mine own country.
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 And Pharaoh said to him, What then dost thou lack with me, that behold, thou desirest to go to thine own country? And he said, Nothing; but in any case let me depart.
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 God stirred him up yet an adversary, Rezon the son of Eliada, who had fled from Hadadezer king of Zobah, his lord.
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 And he collected men to him, and became captain of a band, when David slew them [of Zobah]; and they went to Damascus, and dwelt there, and reigned in Damascus.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 And he was an adversary to Israel all the days of Solomon, besides the mischief that Hadad [did]; and he abhorred Israel, and reigned over Syria.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 And Jeroboam the son of Nebat, an Ephrathite of Zeredah, Solomon's servant (whose mother's name was Zeruah, a widow woman), even he lifted up his hand against the king.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 And this was the cause that he lifted up his hand against the king: Solomon was building Millo, and closing the breach of the city of David his father;
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 and the man Jeroboam was strong and valiant; and Solomon saw the young man that he was industrious, and he made him ruler over all the charge of the house of Joseph.
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 And it came to pass at that time that Jeroboam went out of Jerusalem, and the prophet Ahijah the Shilonite found him in the way; and he had clad himself with a new garment; and they two were alone in the field.
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 Then Ahijah seized the new garment that was on him, and rent it in twelve pieces;
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 and said to Jeroboam, Take thee ten pieces; for thus saith Jehovah the God of Israel: Behold, I will rend the kingdom out of the hand of Solomon, and will give ten tribes to thee;
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 but one tribe shall he have for my servant David's sake, and for Jerusalem's sake, the city which I have chosen out of all the tribes of Israel:
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 because they have forsaken me, and have worshipped Ashtoreth the goddess of the Zidonians, Chemosh the god of the Moabites, and Milcom the god of the children of Ammon, and have not walked in my ways, to do that which is right in my sight, and my statutes and mine ordinances, as David his father.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 But I will not take the whole kingdom out of his hand; for I will make him prince all the days of his life for David my servant's sake, whom I chose, who kept my commandments and my statutes;
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 but I will take the kingdom out of his son's hand, and will give it unto thee, — the ten tribes.
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 And unto his son will I give one tribe, that David my servant may have a lamp always before me in Jerusalem, the city that I have chosen for myself to put my name there.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 And I will take thee, that thou mayest reign over all that thy soul desireth, and thou shalt be king over Israel.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 And it shall be, if thou wilt hearken unto all that I command thee, and wilt walk in my ways, and do that which is right in my sight, in keeping my statutes and my commandments, as David my servant did, that I will be with thee, and build thee a lasting house, as I built for David, and will give Israel unto thee.
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 And I will for this afflict the seed of David, but not for ever.
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 And Solomon sought to kill Jeroboam; and Jeroboam arose and fled into Egypt, to Shishak king of Egypt; and he was in Egypt until the death of Solomon.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 And the rest of the acts of Solomon, and all that he did, and his wisdom, are they not written in the book of the acts of Solomon?
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 And the time that Solomon reigned in Jerusalem over all Israel was forty years.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 And Solomon slept with his fathers, and was buried in the city of David his father; and Rehoboam his son reigned in his stead.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 1 Kings 11 >