< Zechariah 5 >

1 And I turned and lifted up my eyes. And I saw, and behold, a book flying.
Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
2 And he said to me, “What do you see?” And I said, “I see a book flying. Its length is twenty cubits, and its width is ten cubits.”
Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
3 And he said to me, “This is the curse that goes forth over the face of the whole earth. For every thief will be judged, just as it has been written there, and everyone who swears by this, will be judged in like manner.”
Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
4 I will bring it forth, says the Lord of hosts, and it will approach to the house of the thief, and to the house of him who swears falsely by my name, and it will remain in the midst of his house and will consume it, with its wood and its stones.
Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
5 And the angel had departed, who was speaking with me. And he said to me, “Lift up your eyes, and see what this is, that goes forth.”
Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
6 And I said, “What, then, is it?” And he said, “This is a container going forth.” And he said, “This is their eye in all the earth.”
Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
7 And behold, a talent of lead was being carried; and behold, one woman sitting in the middle of the container.
Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
8 And he said, “This is impiety.” And he cast her into the middle of the container, and he sent the weight of lead into its mouth.
Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
9 And I lifted up my eyes and I saw. And behold, two women were departing, and a spirit was in their wings, and they had wings like the wings of a kite, and they lifted up the container between earth and heaven.
Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
10 And I said to the angel who was speaking with me, “Where are they taking the container?”
Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
11 And he said to me, “To a house that may be built for it in the land of Shinar, and so that it may be established and set there upon its own base.”
Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”

< Zechariah 5 >