< Zechariah 10 >

1 Petition before the Lord for rain in the latter time, and the Lord will produce snows and will give showers of rain to them, to each blade in the field.
Ku roƙi Ubangiji yă ba ku ruwa a lokacin bazara; Ubangiji ne yake yin gizagizan hadari. Shi ne yake ba wa mutane yayyafin ruwan sama yana kuma ba da tsire-tsire na fili ga kowa.
2 For the images have been speaking what is useless, and the diviners have seen a lie, and the dreamers have been speaking false hope: they have comforted in vain. For this reason, they have been led away like a flock; they will be afflicted, because they have no shepherd.
Gumaka suna maganganun ruɗu, masu duba suna ganin wahayoyin ƙarya, suna faɗa mafarkan ƙarya suna ba da ta’aziyyar banza. Saboda haka mutane suna yawo kamar tumaki waɗanda suke shan wahala saboda rashin makiyayi.
3 My fury has been kindled over the shepherds, and I will visit upon the he-goats. For the Lord of hosts has visited his flock, the house of Judah, and he has set them like the horse of his glory in the war.
“Ina fushi da makiyayan, zan kuma hukunta shugabannin; gama Ubangiji Maɗaukaki zai lura da garkensa, wato, gidan Yahuda, zai kuma sa su zama kamar doki mai fariya cikin yaƙi.
4 From him will go forth the angle, from him the wooden peg, from him the bow of battle, from him every exactor at the same time.
Daga Yahuda dutsen kusurwa zai fito, daga gare shi za a samu abin kafa tenti, daga gare shi za a sami bakan yaƙi, daga gare shi za a sami kowane mai mulki.
5 And they will be like the strong, trampling the mud of the ways in battle. And they will fight, for the Lord is with them. And the riders of the horses will be confounded.
Tare za su zama kamar mutane masu ƙarfi suna tattake lakar tituna a cikin yaƙi. Domin Ubangiji yana tare da su, za su yi faɗa su kuma yi nasara a kan masu yaƙi a kan dawakai.
6 And I will strengthen the house of Judah, and I will save the house of Joseph, and I will convert them, because I will have mercy on them. And they will be as they were when I had not cast them away. For I am the Lord their God, and I will hear them.
“Zan ƙarfafa gidan Yahuda in kuma ceci gidan Yusuf. Zan maido da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar ban taɓa ƙinsu ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu zan kuma amsa musu.
7 And they will be like the strong of Ephraim, and their heart will rejoice as if by wine, and their sons will see and will rejoice, and their heart will exult in the Lord.
Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi.’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
8 I will whistle for them, and I will gather them together, because I have redeemed them. And I will multiply them, as they had been multiplied before.
Zan ba da alama in kuma tattara su. Ba shakka zan fanshe su; za su yi yawa kamar yadda suke a dā.
9 And I will sow them among the peoples, and from far away they will remember me. And they will live with their sons, and they will return.
Ko da yake na warwatsa su cikin mutane, duk da haka a can ƙasashe masu nisa za su tuna da ni. Su da’ya’yansu za su rayu, za su kuwa komo.
10 And I will lead them back from the land of Egypt, and I will gather them from among the Assyrians, and I will lead them to the land of Gilead and Lebanon, and no place will be left that has not been found by them.
Zan komo da su daga Masar in kuma tattara su daga Assuriya. Zan kawo su Gileyad da Lebanon, har wuri yă kāsa musu.
11 And he will pass over the narrow passage of the sea, and he will strike the waves of the sea, and all the depths of the river will be confounded, and the arrogance of Assyria will be brought low, and the scepter of Egypt will withdraw.
Za su ratsa cikin tekun wahala; zan kwantar da raƙuman teku dukan zurfafan Nilu kuma za su bushe. Za a ƙasƙantar da Assuriya, sandar sarautar Masar kuma za tă rabu da ita.
12 I will strengthen them in the Lord, and they will walk in his name, says the Lord.
Zan ƙarfafa su a cikin Ubangiji kuma a cikin sunansa za su yi tafiya,” in ji Ubangiji.

< Zechariah 10 >