< Zechariah 1 >

1 In the eighth month, in the second year of king Darius, the word of the Lord came to Zechariah the son of Berechiah, the son of Iddo, the prophet, saying:
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 The Lord has become angry over the resentful anger of your fathers.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 And you shall say to them: Thus says the Lord of hosts: Turn to me, says the Lord of hosts, and I will turn to you, says the Lord of hosts.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Do not be like your fathers, to whom the former prophets cried out, saying: Thus says the Lord of hosts: Turn from your evil ways and from your wicked thoughts. But they did not heed, and neither did they pay attention to me, says the Lord.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 Your fathers, where are they? And will the prophets live unceasingly?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 Yet truly my words and my lawfulness, which I entrusted to my servants the prophets, were indeed comprehended by your fathers, and so they were converted, and they said: Just as the Lord of hosts decided to do to us, according to our ways and according to our inventions, so has he done to us.
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 On the twenty-fourth day of the eleventh month, which is called Shevat, in the second year of Darius, the word of the Lord came to Zechariah the son of Berechiah, the son of Iddo, the prophet, saying:
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 I saw by night, and behold, a man riding on a red horse, and he stood among the myrtle trees, which were in the chasm. And behind him were horses: red, speckled, and white.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 And I said, “What are these, my lord?” And the angel, who was speaking with me, said to me, “I will reveal to you what these are.”
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 And the man that stood among the myrtle trees answered and said, “These are they, whom the Lord has sent in order to walk through the earth.”
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 And those who stood among the myrtle trees answered the angel of the Lord, and they said, “We have walked through the earth, and behold, all the earth is inhabited and is at rest.”
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 And the angel of the Lord answered and said, “Lord of hosts, how long will you not have mercy on Jerusalem and on the cities of Judah, with which you have been angry? This is now the seventieth year.”
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 And the Lord answered the angel, who had been speaking with me, good words, consoling words.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 And the angel, who was speaking with me, said to me: Cry out, saying: Thus says the Lord of hosts: I have been zealous for Jerusalem and for Zion with a great zeal.
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 And, with a great anger, I am angry with the wealthy nations. Though I had been angry a little, truly they advanced further in evil.
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 Because of this, thus says the Lord: I will be turned back, towards Jerusalem, with mercies; and my house will be built upon this, says the Lord of hosts. And the building line will be extended over Jerusalem.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 Until then, cry out saying: Thus says the Lord of hosts: Until then, my cities will flow with good things, and, until then, the Lord will comfort Zion, and, until then, he will single out Jerusalem.
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 And I lifted up my eyes, and I saw. And behold: four horns.
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 And I said to the angel, who was speaking with me, “What are these?” And he said to me, “These are the horns that have winnowed Judah and Israel and Jerusalem.”
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 And the Lord showed me four workmen.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 And I said, “What have these come to do?” He spoke, saying, “These are the horns that have winnowed Judah, through every single man, and none of them lifted up his head. And these have come to frighten them away, so as to cast down the horns of the Gentiles, which have lifted up a horn over the land of Judah, so as to scatter it.”
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”

< Zechariah 1 >