< Ruth 4 >

1 Then Boaz went up to the gate, and he sat there. And when he had seen the kinsman passing by, whom he had previously discussed, he spoke to him, calling him by his name, “Pause for a little while, and sit down here.” He turned aside and sat down.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 But Boaz, calling aside ten men among the elders of the city, said to them, “Sit down here.”
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 They settled down, and he spoke to the kinsman, “Naomi, who has returned from the region of the Moabites, is selling part of a field of our brother Elimelech.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 I wanted you to hear this, and to tell you in front of everyone sitting here, including the eldest of my people. If you will take possession of it by the right of kinship, buy it and possess it. But if it displeases you, you should reveal this to me, so that I will know what I have to do. For there is no near kinsman besides you, who is before me, and I am after you.” But he answered, “I will buy the field.”
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 And Boaz said to him, “When buying the field, you are likewise obliged to accept the hand of the woman Ruth, the Moabite, who was the wife of the deceased, so that you may raise up the name of your near kinsman through his posterity.”
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 He answered, “I yield my right of kinship, for I am obliged not to cut off the posterity of my own family. You may make use of my privilege, which I freely declare I will forego.”
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 Yet it was the custom between kinsmen in this former time in Israel, that if at any time one yielded his right to another, so as to confirm his permission, the man took off his shoe and gave it to his neighbor. This was a testimony of concession in Israel.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 And so Boaz said to his kinsman, “Take off your shoe.” And immediately he released it from his foot.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 And he said to the eldest and to all the people, “You are witnesses this day, that I have taken possession of all that belonged to Elimelech and Chilion and Mahlon, and was bequeathed to Naomi.
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 And Ruth, the Moabite, the wife of Mahlon, I have taken in marriage so as to raise up the name of the deceased in his posterity, so that his name will not be cut off from among his family and his brethren and his people. You, I say, are witnesses of this thing.”
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 All the people who were at the gate, along with the eldest, answered, “We are witnesses. May the Lord make this woman, who enters into your house, like Rachel, and Leah, who built up the house of Israel, so that she may be an example of virtue in Ephrathah, and so that her name may be honored in Bethlehem.
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 And may your house be like the house of Perez, whom Tamar bore to Judah, of the offspring which the Lord will give to you from this young woman.”
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 And so Boaz took Ruth, and received her as his wife, and he went in to her, and the Lord granted to her to conceive and bear a son.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 And the women said to Naomi, “Blessed be the Lord, who has not permitted your family to be without a successor, and may his name be called upon in Israel.
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 And now you may have someone to comfort your soul and to care for you in old age, for he is born of your daughter-in-law, who loves you, and this is much better for you, than if you had seven sons.”
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 And taking up the boy, Naomi placed him on her bosom, and she took on the duties of carrying him and nursing him.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 And the women of the near future were congratulating her and saying, “There was a son born to Naomi. They called his name Obed. Here is the father of Jesse, the father of David.”
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 These are the generations of Perez: Perez conceived Hezron,
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 Hezron conceived Aram, Aram conceived Amminadab,
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 Amminadab conceived Nahshon, Nahshon conceived Salmon,
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 Salmon conceived Boaz, Boaz conceived Obed,
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 Obed conceived Jesse, Jesse conceived David.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Ruth 4 >