< Psalms 1 >

1 Blessed is the man who has not followed the counsel of the impious, and has not remained in the way of sinners, and has not sat in the chair of pestilence.
Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
2 But his will is with the law of the Lord, and he will meditate on his law, day and night.
Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
3 And he will be like a tree that has been planted beside running waters, which will provide its fruit in its time, and its leaf will not fall away, and all things whatsoever that he does will prosper.
Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
4 Not so the impious, not so. For they are like the dust that the wind casts along the face of the earth.
Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
5 Therefore, the impious will not prevail again in judgment, nor sinners in the council of the just.
Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
6 For the Lord knows the way of the just. And the path of the impious will pass away.
Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.

< Psalms 1 >