< Psalms 62 >

1 Unto the end. For Jeduthun. A Psalm of David. Will my soul not be subject to God? For from him is my salvation.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 Yes, he himself is my God and my salvation. He is my supporter; I will be moved no more.
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 How is it that you rush against a man? Every one of you puts to death, as if you were pulling down a ruined wall, leaning over and falling apart.
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 So, truly, they intended to reject my price. I ran in thirst. They blessed with their mouth and cursed with their heart.
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 Yet, truly, my soul will be subject to God. For from him is my patience.
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 For he is my God and my Savior. He is my helper; I will not be expelled.
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 In God is my salvation and my glory. He is the God of my help, and my hope is in God.
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 All peoples gathered together: trust in him. Pour out your hearts in his sight. God is our helper for eternity.
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 So, truly, the sons of men are untrustworthy. The sons of men are liars in the scales, so that, by emptiness, they may deceive among themselves.
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 Do not trust in iniquity, and do not desire plunder. If riches flow toward you, do not be willing to set your heart on them.
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 God has spoken once. I have heard two things: that power belongs to God,
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 and that mercy belongs to you, O Lord. For you will repay each one according to his works.
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”

< Psalms 62 >