< Psalms 59 >

1 Unto the end. May you not destroy. Of David, with the inscription of a title, when Saul sent and watched his house, in order to execute him. Rescue me from my enemies, my God, and free me from those who rise up against me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Rescue me from those who work iniquity, and save me from men of blood.
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 For behold, they have seized my soul. The strong have rushed upon me.
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 And it is neither my iniquity, nor my sin, O Lord. I have run and gone directly, without iniquity.
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 Rise up to meet me, and see: even you, O Lord, the God of hosts, the God of Israel. Reach out to visit all nations. Do not take pity on all those who work iniquity.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 They will return toward evening, and they will suffer hunger like dogs, and they will wander around the city.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 Behold, they will speak with their mouth, and a sword is in their lips: “For who has heard us?”
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 And you, O Lord, will laugh at them. You will lead all the Gentiles to nothing.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 I will guard my strength toward you, for you are God, my supporter.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 My God, his mercy will precede me.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 God will oversee my enemies for me. Do not slay them, lest at times my people may forget them. Scatter them by your virtue. And depose them, O Lord, my protector,
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 by the offense of their mouth and by the speech of their lips. And may they be caught in their arrogance. And, for their cursing and lying, they will be made known
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 at the consummation, in the fury of the consummation, and so they will be no more. And they will know that God will rule over Jacob, even to the ends of the earth.
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 They will return toward evening, and they will suffer hunger like dogs, and they will wander around the city.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 They will be dispersed in order to gnaw, and truly, when they will not have been satisfied, they will murmur.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 But I will sing your strength, and I will extol your mercy, in the morning. For you have been my supporter and my refuge in the day of my tribulation.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 To you, my helper, I will sing psalms. For you are God, my supporter. My God is my mercy.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.

< Psalms 59 >