< Psalms 47 >

1 Unto the end. A Psalm for the sons of Korah. All nations, clap your hands. Shout joyfully to God with a voice of exultation.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 For the Lord is exalted and terrible: a great King over all the earth.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 He has subjected the peoples to us and subdued the nations under our feet.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 He has chosen us for his inheritance: the splendor of Jacob, whom he has loved.
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 God ascends with jubilation, and the Lord with the voice of the trumpet.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Sing psalms to our God, sing psalms. Sing psalms to our King, sing psalms.
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 For God is the King of all the earth. Sing psalms wisely.
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 God will reign over the peoples. God sits upon his holy throne.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 The leaders of the peoples have been gathered together by the God of Abraham. For the strong gods of the earth have been exceedingly exalted.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.

< Psalms 47 >