< Psalms 4 >

1 In parts according to verses. A Psalm of David. When I called upon him, the God of my justice heeded me. In tribulation, you have enlarged me. Have mercy on me, and heed my prayer.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
2 Sons of men, how long will you be dull in heart, so that whatever you love is in vain, and whatever you seek is false? (Pause)
Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
3 And know this: the Lord has made wondrous his holy one. The Lord will heed me when I cry out to him.
Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
4 Be angry, and do not be willing to sin. The things that you say in your hearts: be sorry for them on your beds. (Pause)
Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
5 Offer the sacrifice of justice, and hope in the Lord. Many say, “Who reveals to us what is good?”
Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
6 The light of your countenance, Lord, has been sealed upon us. You have given joy to my heart.
Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
7 By the fruit of their grain, wine, and oil, they have been multiplied.
Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
8 In peace itself, I will sleep and I will rest. For you, O Lord, have established me singularly in hope.
Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.

< Psalms 4 >