< Psalms 39 >

1 Unto the end. For Jeduthun himself. A Canticle of David. I said, “I will keep to my ways, so that I will not offend with my tongue.” I posted a guard at my mouth, when a sinner took up a position against me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
2 I was silenced and humbled, and I was quiet before good things, and my sorrow was renewed.
Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
3 My heart grew hot within me, and, during my (meditation) a fire would flare up.
zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
4 I spoke with my tongue, “O Lord, make me know my end, and what the number of my days will be, so that I may know what is lacking to me.”
“Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
5 Behold, you have made my days measurable, and, before you, my substance is as nothing. Yet truly, all things are vanity: every living man.
Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
6 So then, truly man passes by like an image; even so, he is disquieted in vain. He stores up, and he knows not for whom he will gather these things.
“Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
7 And now, what is it that awaits me? Is it not the Lord? And my substance is with you.
“Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
8 Rescue me from all my iniquities. You have handed me over as a reproach to the foolish.
Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
9 I was silenced, and I did not open my mouth, because it was you who acted.
Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
10 Remove your scourges from me.
Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
11 I fall short at corrections from the strength of your hand. For you have chastised man for iniquity. And you have made his soul shrink away like a spider. Nevertheless, it is in vain that any man be disquieted.
Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
12 O Lord, heed my prayer and my supplication. Pay attention to my tears. Do not be silent. For I am a newcomer with you, and a sojourner, just as all my fathers were.
“Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
13 Forgive me, so that I may be refreshed, before I will go forth and be no more.
Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”

< Psalms 39 >