< Psalms 37 >

1 A Psalm of David himself. Do not choose to imitate the malicious; neither should you envy those who work iniquity.
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 For they will quickly wither away like dry grass, and in like manner to kitchen herbs, they will soon droop.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Hope in the Lord and do good, and dwell in the land, and so you shall be pastured with its riches.
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 Delight in the Lord, and he will grant to you the petitions of your heart.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Reveal your way to the Lord, and hope in him, and he will accomplish it.
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 And he will bring forth your justice like the light, and your judgment like the midday.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Be subject to the Lord and pray to him. Do not choose to compete with him who prospers in his way, with the man who does injustice.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Cease from wrath and leave behind rage. Do not choose to imitate the malicious.
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 For those who are malicious will be exterminated. But those who remain with the Lord, these will inherit the land.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 Yet still a little while, and the sinner will not be. And you will search his place and find nothing.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 But the meek shall inherit the earth, and they will delight in the multitude of peace.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 The sinner will observe the just, and he will gnash his teeth over him.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 But the Lord will laugh at him: for he knows in advance that his day will come.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 The sinners have drawn the sword, they have bent their bow, so as to cast down the poor and the needy, so as to massacre the upright of heart.
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Let their sword enter into their own hearts, and let their bow be broken.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 A little is better to the just than the many riches of sinners.
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 For the arms of sinners will be crushed, but the Lord confirms the just.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 The Lord knows the days of the immaculate, and their inheritance will be in eternity.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 They will not be confounded in an evil time; and in days of famine, they will be satisfied:
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 for sinners will perish. Truly, the adversaries of the Lord, soon after they have been honored and exalted, will fade away, in the same way that smoke fades away.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 The sinner will lend and not release, but the just one shows compassion and donates.
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 For those who bless him will inherit the earth, but those who curse him will perish.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 The steps of a man will be directed by the Lord, and he will choose his way.
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 When he falls, he will not be harmed, because the Lord places his hand under him.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 I have been young, and now I am old; and I have not seen the just forsaken, nor his offspring seeking bread.
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 He shows compassion and lends, all day long, and his offspring will be in blessing.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Turn away from evil and do good, and dwell forever and ever.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 For the Lord loves judgment, and he will not abandon his saints. They will be kept safe in eternity. The unjust will be punished, and the offspring of the impious will perish.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 But the just will inherit the earth, and they will dwell upon it forever and ever.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 The mouth of the just one will express wisdom, and his tongue will speak judgment.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 The law of his God is in his heart, and his steps shall not be supplanted.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 The sinner considers the just one and seeks to put him to death.
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 But the Lord will not abandon him into his hands, nor condemn him, when he will be judged.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Wait for the Lord, and keep to his way. And he will exalt you, so as to inherit the land that you may seize. When the sinners will have passed away, then you shall see.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 I have seen the impious over-exalted, and lifted up like the cedars of Lebanon.
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 And I passed by, and behold, he was not. And I sought him, and his place was not found.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Keep to innocence, and gaze upon fairness: because there are allotments for the peaceful man.
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 But the unjust will be destroyed together: the allotments of the impious will pass away.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 But the salvation of the just is from the Lord, and he is their protector in time of tribulation.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 And the Lord will help them and free them. And he will rescue them from sinners and save them, because they have hoped in him.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.

< Psalms 37 >