< Psalms 36 >

1 Unto the end. To the servant of the Lord, David himself. The unjust one has said within himself that he would commit offenses. There is no fear of God before his eyes.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
2 For he has acted deceitfully in his sight, such that his iniquity will be found to be hatred.
Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
3 The words of his mouth are iniquity and deceit. He is unwilling to understand, so that he may act well.
Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
4 He has been considering iniquity on his bed. He has set himself on every way that is not good; moreover, he has not hated evil.
Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
5 Lord, your mercy is in heaven, and your truth is even to the clouds.
Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
6 Your justice is like the mountains of God. Your judgments are a great abyss. Men and beasts, you will save, O Lord.
Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
7 How you have multiplied your mercy, O God! And so the sons of men will hope under the cover of your wings.
Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
8 They will be inebriated with the fruitfulness of your house, and you will give them to drink from the torrent of your enjoyment.
Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
9 For with you is the fountain of life; and within your light, we will see the light.
Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
10 Extend your mercy before those who know you, and your justice to these, who are upright in heart.
Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
11 May arrogant feet not approach me, and may the hand of the sinner not disturb me.
Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
12 In that place, those who work iniquity have fallen. They have been expelled; they were not able to stand.
Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!

< Psalms 36 >