< Psalms 35 >

1 Of David himself. O Lord, judge those who harm me; assail those who attack me.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Take hold of weapons and a shield, and rise up in assistance to me.
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Bring forth the spear, and close in on those who persecute me. Say to my soul, “I am your salvation.”
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Let them be confounded and in awe, who pursue my soul. Let them be turned back and be confounded, who think up evil against me.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 May they become like dust before the face of the wind, and let the Angel of the Lord hem them in.
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 May their way become dark and slippery, and may the Angel of the Lord pursue them.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 For, without cause, they have concealed their snare for me unto destruction. Over nothing, they have rebuked my soul.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 Let the snare, of which he is ignorant, come upon him, and let the deception, which he has hidden, take hold of him: and may he fall into that very snare.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 But my soul will exult in the Lord and delight over his salvation.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 All my bones will say, “Lord, who is like you?” He rescues the needy from the hand of the stronger one, the indigent and the poor from those who plunder him.
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 Unfair witnesses have risen up, interrogating me about things of which I am ignorant.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 They repaid me evil for good, to the deprivation of my soul.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 But as for me, when they were harassing me, I was clothed with haircloth. I humbled my soul with fasting, and my prayer will become my sinews.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 Like a neighbor, and like our brother, so did I please; like one mourning and contrite, so was I humbled.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 And they have been joyful against me, and they joined together. Scourges have been gathered over me, and I was ignorant of it.
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 They have been scattered, yet they were unremorseful. They have tested me. They scoffed at me with scorn. They gnashed their teeth over me.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Lord, when will you look down upon me? Restore my soul from before their malice, my only one from before the lions.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 I will confess to you in a great Church. I will praise you among a weighty people.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 May those who are my unjust adversaries not be glad over me: those who have hated me without cause, and who nod agreement with their eyes.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 For indeed, they spoke peacefully to me; and speaking with passion to the earth, they intended deceit.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 And they opened their mouth wide over me. They said, “Well, well, our eyes have seen.”
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 You have seen, O Lord, do not be silent. Lord, do not depart from me.
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Rise up and be attentive to my judgment, to my cause, my God and my Lord.
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Judge me according to your justice, O Lord, my God, and do not let them be glad over me.
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 Do not let them say in their hearts, “Well, well, to our soul.” Neither let them say, “We have devoured him.”
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Let them blush and be in awe together, those who congratulate at my misfortunes. Let them be clothed with confusion and awe, who speak great things against me.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 Let them exult and rejoice, who wish my justice, and let them ever say, “The Lord be magnified,” who will the peace of his servant.
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 And so my tongue will express your justice: your praise all day long.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.

< Psalms 35 >