< Psalms 3 >

1 A Psalm of David. When he fled from the face of his son, Absalom. Lord, why have those who trouble me been multiplied? Many rise up against me.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Many say to my soul, “There is no salvation for him in his God.” (Pause)
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 But you, Lord, are my supporter, my glory, and the one who raises up my head.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 I have cried out to the Lord with my voice, and he has heard me from his holy mountain. (Pause)
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 I have slept, and I have been stupefied. But I awakened because the Lord has taken me up.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 I will not fear the thousands of people surrounding me. Rise up, Lord. Save me, my God.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 For you have struck all those who oppose me without cause. You have broken the teeth of sinners.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Salvation is of the Lord, and your blessing is upon your people. (Pause)
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)

< Psalms 3 >