< Psalms 29 >

1 A Psalm of David, at the completion of the tabernacle. Bring to the Lord, O sons of God, bring to the Lord the sons of rams.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Bring to the Lord, glory and honor. Bring to the Lord, glory for his name. Adore the Lord in his holy court.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 The voice of the Lord is over the waters. The God of majesty has thundered. The Lord is over many waters.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 The voice of the Lord is in virtue. The voice of the Lord is in magnificence.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 The voice of the Lord shatters the cedars. And the Lord will shatter the cedars of Lebanon.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 And it will break them into pieces, like a calf of Lebanon, and in the same way as the beloved son of the single-horned beast.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 The voice of the Lord cuts through the flame of fire.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 The voice of the Lord shakes the desert. And the Lord will quake the desert of Kadesh.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 The voice of the Lord is preparing the stags, and he will reveal the dense woods. And in his temple, all will speak his glory.
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 The Lord causes the great flood to dwell. And the Lord will sit as King in eternity.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 The Lord will give virtue to his people. The Lord will bless his people in peace.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Psalms 29 >