< Psalms 22 >

1 Unto the end. For the tasks of early morning. A Psalm of David. O God, my God, look upon me. Why have you forsaken me? Far from my salvation are the words of my offenses.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 My God, I will cry out by day, and you will not heed, and by night, and it will not be foolishness for me.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 But you dwell in holiness, O Praise of Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 In you, our fathers have hoped. They hoped, and you freed them.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 They cried out to you, and they were saved. In you, they hoped and were not confounded.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 But I am a worm and not a man: a disgrace among men, and an outcast of the people.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 All those who saw me have derided me. They have spoken with the lips and shook the head.
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 He has hoped in the Lord, let him rescue him. Let him save him because he chooses him.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 For you are the one who has drawn me out of the womb, my hope from the breasts of my mother.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 I have been thrown upon you from the womb; from the womb of my mother, you are my God.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Do not depart from me. For tribulation is near, since there is no one who may help me.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Many calves have surrounded me; fat bulls have besieged me.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 They have opened their mouths over me, just like a lion seizing and roaring.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 And so, I have been poured out like water, and all my bones have been scattered. My heart has become like wax, melting in the midst of my chest.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 My strength has dried up like clay, and my tongue has adhered to my jaws. And you have pulled me down, into the dust of death.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 For many dogs have surrounded me. The council of the malicious has besieged me. They have pierced my hands and feet.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 They have numbered all my bones. And they have examined me and stared at me.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 They divided my garments among them, and over my vestment, they cast lots.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 But you, O Lord, do not take your help far from me; be attentive to my defense.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 O God, rescue my soul from the spear, and my only one from the hand of the dog.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Save me from the mouth of the lion, and my humility from the horns of the single-horned beast.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 I will declare your name to my brothers. In the midst of the Church, I will praise you.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 You who fear the Lord, praise him. All the offspring of Jacob, glorify him.
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 May all the offspring of Israel fear him. For he has neither spurned nor despised the pleas of the poor. Neither has he turned his face away from me. And when I cried out to him, he heeded me.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 My praise is with you, within a great church. I will pay my vows in the sight of those who fear him.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 The poor will eat and be satisfied, and those who yearn for the Lord will praise him. Their hearts will live forever and ever.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 All the ends of the earth will remember, and they will be converted to the Lord. And all the families of the Gentiles will adore in his sight.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 For the kingdom belongs to the Lord, and he will have dominion over the Gentiles.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 All the fat of the earth have gnashed their teeth, and they have adored. In his sight, they will fall down, all those who descend to the ground.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 And my soul will live for him, and my offspring will serve him.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 There will be announced for the Lord a future generation, and the heavens will announce his justice to a people who will be born, whom the Lord has made.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Psalms 22 >