< Psalms 17 >

1 A Prayer of David. Lord, listen to my justice, attend to my supplication. Pay attention to my prayer, which is not from deceitful lips.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Let my judgment proceed from your presence. Let your eyes behold fairness.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 You have tested my heart and visited it by night. You have examined me by fire, and iniquity has not been found in me.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 Therefore, may my mouth not speak the works of men. I have kept to difficult ways because of the words of your lips.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Perfect my steps in your paths, so that my footsteps may not be disturbed.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 I have cried out because you, O God, have listened to me. Incline your ear to me and heed my words.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Make your mercies wonderful, for you save those who hope in you.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 From those who resist your right hand, preserve me like the pupil of your eye. Protect me under the shadow of your wings,
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 from the face of the impious who have afflicted me. My enemies have surrounded my soul.
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 They have concealed their fatness; their mouth has been speaking arrogantly.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 They have cast me out, and now they have surrounded me. They have cast their eyes down to the earth.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 They have taken me, like a lion ready for the prey, and like a young lion dwelling in hiding.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Rise up, O Lord, arrive before him and displace him. Deliver my soul from the impious one: your spear from the enemies of your hand.
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 Lord, divide them from the few of the earth in their life. Their gut has been filled from your hidden stores. They have been filled with sons, and they have bequeathed to their little ones the remainder.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 But as for me, I will appear before your sight in justice. I will be satisfied when your glory appears.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalms 17 >