< Psalms 145 >

1 The Praise of David himself. I will extol you, O God, my king. And I will bless your name, in this time and forever and ever.
Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
2 Throughout every single day, I will bless you. And I will praise your name, in this time and forever and ever.
Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
3 The Lord is great and exceedingly praiseworthy. And there is no end to his greatness.
Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
4 Generation after generation will praise your works, and they will declare your power.
Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
5 They will tell of the magnificent glory of your sanctity. And they will discourse of your wonders.
Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
6 And they will talk about the virtue of your terrible acts. And they will describe your greatness.
Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
7 They will shout about the memory of your abundant sweetness. And they will exult in your justice.
Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
8 The Lord is compassionate and merciful, patient and full of mercy.
Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
9 The Lord is sweet to all things, and his compassion is upon all his works.
Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
10 O Lord, may all your works confess to you, and let your holy ones bless you.
Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
11 They will speak of the glory of your kingdom, and they will declare your power,
Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
12 so as to make known to the sons of men your power and the glory of your magnificent kingdom.
saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
13 Your kingdom is a kingdom for all ages, and your dominion is with all, from generation to generation. The Lord is faithful in all his words and holy in all his works.
Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
14 The Lord lifts up all who have fallen down, and he sets upright all who have been thrown down.
Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
15 O Lord, all eyes hope in you, and you provide their food in due time.
Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
16 You open your hand, and you fill every kind of animal with a blessing.
Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
17 The Lord is just in all his ways and holy in all his works.
Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
18 The Lord is near to all who call upon him, to all who call upon him in truth.
Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
19 He will do the will of those who fear him, and he will heed their supplication and accomplish their salvation.
Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
20 The Lord watches over all who love him. And he will destroy all sinners.
Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
21 My mouth will speak the praise of the Lord, and may all flesh bless his holy name, in this time and forever and ever.
Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.

< Psalms 145 >