< Psalms 143 >

1 A Psalm of David, when his son Absalom was pursuing him. O Lord, hear my prayer. Incline your ear to my supplication in your truth. Heed me according to your justice.
Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, ka ji addu’ata, ka saurari kukata don neman jinƙai; cikin amincinka da adalcinka ka amsa mini.
2 And do not enter into judgment with your servant. For all the living will not be justified in your sight.
Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari’a, gama babu wani mai rai da yake adali a gabanka.
3 For the enemy has pursued my soul. He has lowered my life to the earth. He has stationed me in darkness, like the dead of ages past.
Abokin gāba yana fafarata, ya murƙushe ni har ƙasa; ya sa ina zama a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun tuni.
4 And my spirit has been in anguish over me. My heart within me has been disturbed.
Ta haka ƙarfina ya ƙare a cikina zuciyata ta damu ƙwarai.
5 I have called to mind the days of antiquity. I have been meditating on all your works. I have meditated on the workings of your hands.
Na tuna da kwanakin baya na yi tunani a kan dukan ayyukanka na kuma lura da abin da hannuwanka suka yi.
6 I have extended my hands to you. My soul is like a land without water before you.
Na buɗe hannuwana gare ka; raina yana jin ƙishinka kamar busasshiyar ƙasa. (Sela)
7 O Lord, heed me quickly. My spirit has grown faint. Do not turn your face away from me, lest I become like those who descend into the pit.
Ka amsa mini da sauri, ya Ubangiji; ƙarfina ya ƙare. Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni in ba haka ba zan zama kamar waɗanda suka gangara zuwa rami.
8 Make me hear your mercy in the morning. For I have hoped in you. Make known to me the way that I should walk. For I have lifted up my soul to you.
Bari safiya ta kawo mini maganar ƙaunarka marar ƙarewa, gama na sa zuciyata a gare ka. Ka nuna mini hanyar da zan bi, gama a gare ka na miƙa raina.
9 O Lord, rescue me from my enemies. I have fled to you.
Ka cece ni daga abokan gābana, ya Ubangiji, gama na ɓoye kaina a gare ka.
10 Teach me to do your will. For you are my God. Your good Spirit will lead me into the righteous land.
Ka koya mini in yi nufinka, gama kai ne Allahna; bari nagarin Ruhunka yă bi da ni a ƙasar da ba gargaɗa.
11 For the sake of your name, O Lord, you will revive me in your fairness. You will lead my soul out of tribulation.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka kiyaye raina; a cikin adalcinka, ka fid da ni daga wahala.
12 And you will scatter my enemies in your mercy. And you will destroy all those who afflict my soul. For I am your servant.
A cikin ƙaunarka marar ƙarewa, ka rufe bakunan abokan gābana; ka hallaka dukan maƙiyana, gama ni bawanka ne.

< Psalms 143 >