< Psalms 132 >

1 A Canticle in steps. O Lord, remember David and all his meekness,
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 how he swore to the Lord, how he made a vow to the God of Jacob:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 I shall not enter into the tabernacle of my house, nor climb into the bed where I lie down;
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 I shall not give sleep to my eyes, nor slumber to my eyelids
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 and rest to my temples, until I find a place for the Lord, a tabernacle for the God of Jacob.
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Behold, we heard of it in Ephrathah. We discovered it in the fields of the forest.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 We will enter into his tabernacle. We will adore in the place where his feet stood.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Rise up, O Lord, into your resting place. You and the ark of your sanctification.
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Let your priests be clothed with justice, and let your saints exult.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 For the sake of your servant David, do not turn away the face of your Christ.
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 The Lord has sworn the truth to David, and he will not disappoint: I will set upon your throne from the fruit of your lineage.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 If your sons will keep my covenant and these, my testimonies, which I will teach to them, then their sons will sit upon your throne even forever.
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 For the Lord has chosen Zion. He has chosen it as his dwelling place.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 This is my resting place, forever and ever. Here I will dwell, for I have chosen it.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 When blessing, I will bless her widow. I will satisfy her poor with bread.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 I will clothe her priests with salvation, and her saints will rejoice with great joy.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 There, I will produce a horn to David. There, I have prepared a lamp for my Christ.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 I will clothe his enemies with confusion. But my sanctification will flourish over him.
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”

< Psalms 132 >