< Psalms 112 >

1 Alleluia. Of the return of Haggai and Zachariah. Blessed is the man who fears the Lord. He will prefer his commandments exceedingly.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 His offspring will be powerful on the earth. The generation of the upright will be blessed.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Glory and wealth will be in his house, and his justice shall remain from age to age.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 For the upright, a light has risen up in the darkness. He is merciful and compassionate and just.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 Pleasing is the man who shows mercy and lends. He will order his words with judgment.
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 For he will not be disturbed in eternity.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 The just one will be an everlasting memorial. He will not fear a report of disasters. His heart is prepared to hope in the Lord.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 His heart has been confirmed. He will not be disturbed, until he looks down upon his enemies.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 He has distributed, he has given to the poor. His justice shall remain from age to age. His horn shall be exalted in glory.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 The sinner will see and become angry. He will gnash his teeth and waste away. The desire of sinners will perish.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Psalms 112 >