< Psalms 104 >

1 To David himself. Bless the Lord, O my soul. O Lord my God, you are exceedingly great. You have clothed yourself with confession and beauty;
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
2 you are dressed with light like a garment, while you stretch out heaven like a tent.
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
3 You cover its heights with water. You set the clouds as your stairs. You walk upon the wings of the winds.
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
4 You make your Angels a breath of life, and your ministers a burning fire.
Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
5 You founded the earth upon its stable base. It will not be bent from age to age.
Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
6 The abyss, like a garment, is its clothing. The waters will remain standing above the mountains.
Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
7 At your rebuke, they will flee. At the voice of your thunder, they will dread.
Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
8 The mountains ascend, and the plains descend, to the place which you have founded for them.
suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
9 You have set a limit that they will not cross. And they will not return to cover the earth.
Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
10 You spring forth fountains in steep valleys. The waters will cross through the midst of the mountains.
Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
11 All the wild beasts of the field will drink. The wild donkeys will anticipate in their thirst.
Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
12 Above them, the flying things of the air will dwell. From the midst of the rocks, they will utter voices.
Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
13 You irrigate the mountains from your heights. The earth will be satiated from the fruit of your works,
Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
14 producing grass for cattle and herbs for the service of men. So may you draw bread from the earth,
Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
15 and wine, in order to cheer the heart of man. Then he may gladden his face with oil, and bread will confirm the heart of man.
ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
16 The trees of the field will be saturated, along with the cedars of Lebanon, which he planted.
Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
17 There, the sparrows will make their nests. The leader of them is the house of the heron.
A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
18 The heights of the hills are for the deer; the rock is a refuge for the hedgehog.
Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
19 He has made the moon for seasons; the sun knows its setting.
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20 You appointed darkness, and it has become night; all the beasts of the forest will cross through it.
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21 The young lions will roar, while searching for and seizing their meal from God.
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22 The sun arose, and they were gathered together; and in their dens, they will lie down together.
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23 Man will go forth to his work and to his activities, until the evening.
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
24 How great are your works, O Lord! You have made all things in wisdom. The earth has been filled with your possessions.
Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
25 This sea is great and its hands are spacious. There are creeping things without number: the small animals with the great.
Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
26 There, the ships will pass by this sea-serpent that you have formed to mock them.
A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
27 All these expect you to give them food in due time.
Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
28 What you give to them, they will gather. When you open your hand, they will all be filled with goodness.
Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
29 But if you turn your face away, they will be disturbed. You will take away their breath, and they will fail, and they will return to their dust.
Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
30 You will send forth your Spirit, and they will be created. And you will renew the face of the earth.
Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
31 May the glory of the Lord be for all ages. The Lord will rejoice in his works.
Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
32 He considers the earth, and he makes it tremble. He touches the mountains, and they smoke.
shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
33 I will sing to the Lord with my life. I will sing psalms to my God, as long as I am.
Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
34 May my speech be pleasing to him. Truly, I will take delight in the Lord.
Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
35 Let sinners fade away from the earth, along with the unjust, so that they may not be. Bless the Lord, O my soul.
Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.

< Psalms 104 >