< Psalms 102 >

1 The prayer of the pauper, when he was anxious, and so he poured out his petition in the sight of the Lord. O Lord, hear my prayer, and let my outcry reach you.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Do not turn your face away from me. In whatever day that I am in trouble, incline your ear to me. In whatever day that I will call upon you, heed me quickly.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 For my days have faded away like smoke, and my bones have dried out like firewood.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 I have been cut down like hay, and my heart has withered, for I had forgotten to eat my bread.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Before the voice of my groaning, my bone has adhered to my flesh.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 I have become like a pelican in solitude. I have become like a night raven in a house.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 I have kept vigil, and I have become like a solitary sparrow on a roof.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 All day long my enemies reproached me, and those who praised me swore oaths against me.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 For I chewed on ashes like bread, and I mixed weeping into my drink.
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 By the face of your anger and indignation, you lifted me up and threw me down.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 My days have declined like a shadow, and I have dried out like hay.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 But you, O Lord, endure for eternity, and your memorial is from generation to generation.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 You will rise up and take pity on Zion, for it is time for its mercy, for the time has come.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 For its stones have pleased your servants, and they will take pity on its land.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 And the Gentiles will fear your name, O Lord, and all the kings of the earth your glory.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 For the Lord has built up Zion, and he will be seen in his glory.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 He has noticed the prayer of the humble, and he has not despised their petition.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Let these things be written in another generation, and the people who will be created will praise the Lord.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 For he has gazed from his high sanctuary. From heaven, the Lord has beheld the earth.
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 So may he hear the groans of those in shackles, in order that he may release the sons of the slain.
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 So may they announce the name of the Lord in Zion and his praise in Jerusalem:
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 while the people convene, along with kings, in order that they may serve the Lord.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 He responded to him in the way of his virtue: Declare to me the brevity of my days.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Do not call me back in the middle of my days: your years are from generation to generation.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 In the beginning, O Lord, you founded the earth. And the heavens are the work of your hands.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 They will perish, but you remain. And all will grow old like a garment. And, like a blanket, you will change them, and they will be changed.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Yet you are ever yourself, and your years will not decline.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 The sons of your servants will live, and their offspring will be guided aright in every age.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Psalms 102 >