< Psalms 101 >

1 A Psalm of David himself. I will sing mercy and judgment to you, O Lord. I will sing psalms.
Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
2 And I will have understanding within the immaculate way, when you will draw near to me. I wandered about in the innocence of my heart, in the midst of my house.
Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
3 I will not display any unjust thing before my eyes. I have hated those carrying out betrayals.
Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
4 The perverse heart did not adhere to me. And the malignant, who turned away before me, I would not recognize.
Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
5 The one who secretly detracted his neighbor, this one I pursued. The one with an arrogant eye and an insatiable heart, with that one I would not eat.
Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
6 My eyes looked toward the faithful of the earth, to sit with me. The one walking in the immaculate way, this one ministered to me.
Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
7 He who has acted arrogantly will not dwell in the midst of my house. He who has spoken iniquity was not guided with the sight of my eyes.
Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
8 In the morning, I executed all the sinners of the earth, so that I might scatter all the workers of iniquity from the city of the Lord.
Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.

< Psalms 101 >