< Proverbs 3 >

1 My son, do not forget my law, but let your heart guard my precepts.
Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
2 For they shall set before you length of days, and years of life, and peace.
gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
3 Let not mercy and truth abandon you: encircle them around your throat, and inscribe them on the tablets of your heart.
Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 And so shall you discover grace and good discipline, in the sight of God and men.
Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
5 Have confidence in the Lord with all your heart, and do not depend upon your own prudence.
Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
6 In all your ways, consider him, and he himself will direct your steps.
cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
7 Do not seem wise to yourself. Fear God, and withdraw from evil.
Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
8 Certainly, it shall be health to your navel, and refreshment to your bones.
Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
9 Honor the Lord with your substance, and give to him from the first of all your fruits,
Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
10 and then your storehouses will be filled with abundance, and your presses shall overflow with wine.
ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
11 My son, do not discard the discipline of the Lord, and do not fall away when you are corrected by him.
Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
12 For whomever the Lord loves, he corrects, and just as a father does with a son, he wins him over.
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
13 Blessed is the man who finds wisdom and who advances to prudence.
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14 Her acquisition is better than trading in silver, and her fruit is better than the first and purest gold.
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15 She is more precious than all riches, and all that can be desired cannot prevail in comparison to her.
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16 Length of days is at her right hand, and at her left hand is wealth and glory.
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17 Her ways are beautiful ways, and all her paths are peaceful.
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18 She is a tree of life to those who overtake her, and he who shall take hold of her is blessed.
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19 The Lord founded the earth on wisdom. He secured the heavens with prudence.
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20 By his wisdom, the abyss erupted and the clouds increased with dew.
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21 My son, let not these things move away from your eyes. Preserve law as well as counsel.
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22 And so shall there be life in your soul and grace in your voice.
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23 Then you shall walk confidently in your way, and your feet will not stumble.
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24 When you slumber, you shall not fear. When you rest, your sleep also will be sweet.
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25 Do not fear unexpected terror, nor the power of the impious falling upon you.
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26 For the Lord will be at your side, and he will guard your feet, so that you may not be seized.
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
27 Do not prevent him who is able from doing good. When you are able, do good yourself too.
Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
28 Do not say to your friend: “Go away, and then return. Tomorrow I will give to you.” When you are able to do so, give in the present.
Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
29 Do not undertake evil against your friend, even though he has trust in you.
Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
30 Do not contend against a man without cause, even though he has done no evil to you.
Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
31 Do not rival an unjust man, and do not imitate his ways.
Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
32 For everyone who ridicules is an abomination to the Lord, and his communication is for the simple.
Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
33 Destitution in the house of the impious is from the Lord. But the habitations of the just shall be blessed.
La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
34 He will ridicule those who ridicule, but he will bestow grace upon the mild.
Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
35 The wise will possess glory. The exaltation of the foolish is disgraceful.
Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.

< Proverbs 3 >