< Proverbs 24 >

1 Do not imitate evil men, nor desire to be among them.
Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
2 For their mind meditates on robberies, and their lips speak deceptions.
gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
3 By wisdom shall a house be built, and by prudence shall it be strengthened.
Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
4 By doctrine, the storerooms shall be filled with every substance that is precious and most beautiful.
ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
5 A wise man is strong, and a well-taught man is robust and valiant.
Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
6 For war is undertaken in an orderly manner, and safety shall be where there are many counsels.
don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
7 Wisdom is beyond the foolish; at the gate he will not open his mouth.
Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
8 Whoever intends to do evil shall be called foolish.
Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
9 The intention of the foolish is sin. And the detractor is an abomination among men.
Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
10 If you despair, being weary in the day of anguish, your strength will be diminished.
In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
11 Rescue those who are led away to death. And do not cease from delivering those who are dragged away to a violent death.
Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
12 If you would say: “I do not have sufficient strength.” He who inspects the heart, the same one understands, and nothing slips past the one who preserves your soul. And he shall repay a man according to his works.
In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
13 My son, eat honey, because it is good, and the honeycomb, because it is so sweet to your throat.
Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
14 So, too, is the doctrine of wisdom to your soul. When you have found it, you will have hope in the end, and your hope shall not perish.
Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
15 Do not lie in wait, and do not seek impiety in the house of the just, nor spoil his rest.
Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
16 For the just one will fall seven times, and he shall rise again. But the impious will fall into evil.
gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
17 When your enemy will fall, do not be glad, and do not let your heart exult in his ruin,
Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
18 lest perhaps the Lord see, and it displease him, and he may take away his wrath from him.
in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
19 Do not contend with the most wicked, and do not be a rival to the impious.
Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
20 For the evil hold no hope in the future, and the lamp of the impious will be extinguished.
gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
21 My son, fear the Lord, as well as the king. And do not mingle with detractors.
Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
22 For their perdition shall rise up suddenly. And who knows what ruin will be for each of them?
gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
23 Likewise, these things are for the wise. It is not good to base judgment on knowledge of character.
Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
24 Those who say to the impious, “You are just,” shall be cursed by the people, and the tribes shall detest them.
Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
25 Those who argue against the impious shall be praised, and a blessing shall come upon them.
Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
26 He shall kiss the lips, who responds with upright words.
Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
27 Prepare your outdoor work, and diligently cultivate your field, so that afterward, you may build your house.
Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
28 Do not be a witness without cause against your neighbor. And do not mislead anyone with your lips.
Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
29 Do not say, “I will do to him as he has done to me.” I will repay each one according to his work.
Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
30 I passed by the field of a lazy man, and by the vineyard of a foolish man,
Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
31 and behold, it was entirely filled with nettles, and thorns had covered its surface, and the stonewall was destroyed.
ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
32 When I had seen this, I laid it up in my heart, and by this example, I received discipline.
Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
33 You will sleep a little,” I said. “You will slumber briefly. You will fold your hands a little, so as to rest.
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
34 And destitution will overtake you like a runner, and begging will overtake you like an armed man.”
sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.

< Proverbs 24 >