< Proverbs 21 >

1 Just as with the dividing of the waters, so also is the heart of the king in the hand of the Lord. He shall bend it whichever way he wills.
A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
2 Every way of a man seems right to himself. But the Lord weighs hearts.
Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
3 To do mercy and judgment is more pleasing to the Lord than sacrifices.
Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
4 To lift up the eyes is to enlarge the heart. The lamp of the impious is sin.
Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
5 The intentions of the robust continually bring forth abundance. But all the lazy are continually in need.
Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
6 Whoever gathers treasures by a lying tongue is vain and heartless. And he will stumble into the snares of death.
Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
7 The robberies of the impious will drag them down, because they were not willing to do judgment.
Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
8 The perverse way of a man is foreign. But whoever is pure: his work is upright.
Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
9 It is better to sit in a corner of the attic, than with a contentious woman and in a shared house.
Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
10 The soul of the impious desires evil; he will not take pity on his neighbor.
Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
11 When the pestilent is punished, a little one will become wiser. And if he pursues what is wise, he will receive knowledge.
Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
12 The just thinks carefully about the house of the impious, so that he may draw the impious away from evil.
Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
13 Whoever blocks his ears to the outcry of the poor shall also cry out himself, and he will not be heeded.
In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
14 A surprise gift extinguishes anger. And a gift concealed in the bosom extinguishes the greatest indignation.
Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
15 It is gladness for the just to do judgment; and it is dread for those who work iniquity.
Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
16 A man who wanders astray from the way of doctrine will linger in the company of the giants.
Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
17 Whoever loves a feast will be in deprivation. Whoever loves wine and fatness will not be enriched.
Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
18 The impious is given over instead of the just, and the iniquitous is given over in place of the upright.
Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
19 It is better to live in a deserted land, than with a quarrelsome and emotional woman.
Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
20 There is desirable treasure, as well as oil, in the habitations of the just. And the imprudent man will waste it.
A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
21 Whoever follows justice and mercy shall discover life, justice, and glory.
Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
22 The wise has ascended the city of the strong, and he has torn down the bulwark of its confidence.
Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
23 Whoever guards his mouth and his tongue guards his soul from anguish.
Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
24 A proud and arrogant one is also called ignorant, if he, in anger, acts according to pride.
Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
25 Desires kill the lazy, for his hands are not willing to work at all.
Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
26 He covets and desires all day long. But whoever is just shall distribute and shall not cease.
Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
27 The sacrifices of the impious are abominable, because they are offered out of wickedness.
Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
28 A lying witness will perish. An obedient man shall speak of victory.
Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
29 The impious man insolently hardens his face. But whoever is upright corrects his own way.
Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
30 There is no wisdom, there is no prudence, there is no counsel, which is against the Lord.
Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
31 The horse is prepared for the day of battle. But the Lord bestows salvation.
Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.

< Proverbs 21 >