< Proverbs 15 >

1 A mild response shatters anger. But a harsh word stirs up fury.
Amsa da tattausar harshe kan kwantar da fushi, amma magana da kakkausan harshe kan kuta fushi.
2 The tongue of the wise adorns knowledge. But the mouth of the senseless gushes with foolishness.
Harshen mai hikima kan yi zance mai kyau a kan sani, amma bakin wawa kan fitar da wauta.
3 In every place, the eyes of the Lord consider good and evil.
Idanun Ubangiji suna a ko’ina, suna lura da masu aikata mugunta da masu aikata alheri.
4 A peaceful tongue is a tree of life. But that which is immoderate will crush the spirit.
Harshen da ya kawo warkarwa shi ne itacen rai, amma harshe mai ƙarya kan ragargaza zuciya.
5 A fool laughs at the discipline of his father. But whoever preserves rebukes will become astute. In abundant justice, there is very great virtue. But the intentions of the impious will be eradicated.
Wawa yakan ƙi kulawa da horon da mahaifinsa yake masa, amma duk wanda ya yarda da gyara kan nuna azanci.
6 The house of the just has very great strength. And in the fruits of the impious, there is disorder.
Gidan adali yana da dukiya mai yawa, amma albashin mugaye kan kawo musu wahala.
7 The lips of the wise shall disseminate knowledge. The heart of the foolish will be dissimilar.
Leɓunan masu hikima sukan baza sani; ba haka zukatan wawaye suke ba.
8 The sacrifices of the impious are abominable to the Lord. The vows of the just are appeasing.
Ubangiji yana ƙyamar hadayar mugaye, amma addu’ar masu aikata gaskiya kan sa ya ji daɗi.
9 The way of the impious is an abomination to the Lord. Whoever pursues justice is loved by him.
Ubangiji yana ƙin hanyar mugaye amma yana ƙaunar waɗanda suke neman adalci.
10 Doctrine is evil to those who abandon the way of life. Whoever hates correction shall die.
Horo mai tsanani yana jiran duk wanda ya bar hanya; wanda ya ƙi gyara zai mutu.
11 Hell and perdition are in the sight of the Lord. How much more the hearts of the sons of men! (Sheol h7585)
Mutuwa da Hallaka suna nan a fili a gaban Ubangiji, balle fa zukatan mutane! (Sheol h7585)
12 He who corrupts himself does not love the one who afflicts him, nor will he step toward the wise.
Mai yin ba’a yakan ƙi gyara; ba zai nemi shawara mai hikima ba.
13 A rejoicing heart gladdens the face. But by the grief of the soul, the spirit is cast down.
Zuciya mai farin ciki kan sa fuska tă yi haske, amma ciwon zuciya kan ragargaza rai.
14 The heart of the wise seeks doctrine. And the mouth of the foolish feeds on ignorance.
Zuciya mai la’akari kan nemi sani, amma bakin wawa wauta ce ke ciyar da shi.
15 All the days of the poor are evil. A secure mind is like a continual feast.
Dukan kwanakin mutumin da ake danniya fama yake yi, amma zuciya mai farin ciki yana yin biki kullum.
16 Better is a little with the fear of the Lord, than great treasures and dissatisfaction.
Gara a kasance da kaɗan da tsoron Ubangiji da a kasance da arziki mai yawa game da wahala.
17 It is better to be called to vegetables with charity, than to a fatted calf with hatred.
Gara a ci abincin kayan ganye inda akwai ƙauna da a ci kiwotaccen saniya inda ƙiyayya take.
18 A short-tempered man provokes conflicts. Whoever is patient tempers those who are stirred up.
Mutum mai zafin rai kan kawo faɗa, amma mutum mai haƙuri kan kwantar da faɗa.
19 The way of the slothful is like a hedge of thorns. The way of the just is without offense.
An tare hanyar rago da ƙayayyuwa, amma hanyar mai aikata gaskiya buɗaɗɗiyar hanya ce.
20 A wise son gladdens the father. But the foolish man despises his mother.
Ɗa mai hikima kan kawo farin ciki wa mahaifinsa, amma wawa yakan rena mahaifiyarsa.
21 Folly is gladness to the foolish. And the prudent man sets his own steps in order.
Wauta kan sa mutum marar azanci ya yi farin ciki, amma mai basira kan kiyaye abin da yake yi daidai.
22 Intentions dissipate where there is no counsel. Yet truly, they are confirmed where there are many counselors.
Shirye-shirye sukan lalace saboda rashin neman shawara, amma tare da mashawarta masu yawa za su yi nasara.
23 A man rejoices in the verdict of his own mouth. And a word at the right time is best.
Mutum yakan yi farin ciki a ba da amsar da take daidai, kuma ina misali a yi magana a lokacin da ya dace!
24 The path of life is for the wise above, so that he may turn away from the end of Hell. (Sheol h7585)
Hanyar rai na yin jagora ya haura wa masu hikima don ta kiyaye shi daga gangarawa zuwa kabari. (Sheol h7585)
25 The Lord will demolish the house of the arrogant. And He will make firm the borders of the widow.
Ubangiji yakan rushe gidan mai girman kai amma yakan kiyaye iyakokin gwauruwa daidai.
26 Evil intentions are an abomination to the Lord. And pure conversation, most beautiful, shall be confirmed by him.
Ubangiji yana ƙyamar tunanin mugaye, amma waɗanda suke da tunani masu tsabta yakan ji daɗinsu.
27 Whoever pursues avarice disturbs his own house. But whoever hates bribes shall live. Through mercy and faith, sins are purged. But through the fear of the Lord, each one turns aside from evil.
Mutum mai haɗama kan kawo wahala ga iyalinsa, amma wanda yake ƙin cin hanci zai rayu.
28 The mind of the just meditates on obedience. The mouth of the impious overflows with evils.
Zuciyar mai adalci takan auna amsoshinta, amma bakin mugu yakan fitar da mugunta.
29 The Lord is distant from the impious. And he will heed the prayers of the just.
Ubangiji yana nesa da mugaye amma yakan ji addu’ar adalai.
30 The light of the eyes rejoices the soul. A good reputation fattens the bones.
Fuska mai fara’a takan kawo farin ciki ga zuciya, kuma labari mai daɗi na kawo lafiya ga ƙasusuwa.
31 The ear that listens to the reproofs of life shall abide in the midst of the wise.
Duk wanda ya mai da hankali sa’ad da ake tsawata masa ba zai kasance dabam a cikin masu hikima ba.
32 Whoever rejects discipline despises his own soul. But whoever agrees to correction is a possessor of the heart.
Duk waɗanda suka ƙi horon sun rena kansu ke nan, amma duk waɗanda sun yarda da gyara sukan ƙara basira.
33 The fear of the Lord is the discipline of wisdom. And humility precedes glory.
Tsoron Ubangiji yakan koya wa mutum hikima, kuma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.

< Proverbs 15 >