< Proverbs 1 >

1 The parables of Solomon, son of David, king of Israel,
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 in order to know wisdom and discipline,
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 to understand words of prudence, and to accept the instruction of doctrine, justice and judgment, and equity,
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 so as to give discernment to little ones, knowledge and understanding to adolescents.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 By listening, the wise shall become wiser and the intelligent shall possess governments.
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 He shall turn his soul to a parable and to its interpretation, to the words of the wise and their enigmas.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 The fear of the Lord is the beginning of wisdom. The foolish despise wisdom as well as doctrine.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Listen, my son, to the discipline of your father, and forsake not the law of your mother,
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 so that grace may be added to your head and a collar to your neck.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 My son, if sinners should entice you, do not consent to them.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 If they should say: “Come with us. We will lie in wait for blood. We will lay traps against the innocent, without cause.
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 Let us swallow him alive, like Hell, and whole, like one descending into the pit. (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 We will discover every precious substance. We will fill our houses with spoils.
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Cast your lot with us. One purse will be for us all.”
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 My son, do not walk with them. Preclude your feet from their paths.
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 For their feet rush to evil, and they hurry to shed blood.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 But a net is thrown in vain before the eyes of those who have wings.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 Likewise, they lie in ambush against their own blood, and they undertake deceits against their own souls.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Thus, the ways of all those who are greedy seize the souls of those who possess.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 Wisdom forewarns far and wide; she bestows her voice in the streets.
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 She cries out at the head of crowds; at the entrance of the gates of the city, she offers her words, saying:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 “Little ones, how long will you choose to be childish, and how long will the foolish desire what is harmful to themselves, and how long will the imprudent hate knowledge?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Be converted by my correction. Lo, I will offer my spirit to you, and I will reveal my words to you.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 For I called, and you refused. I extended my hand, and there was no one who watched.
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 You have despised all my counsels, and you have neglected my rebukes.
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 Similarly, I will ridicule you at your demise, and I will mock you, when that which you feared shall overcome you.
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 When sudden calamity rushes upon you, and your demise advances like a tempest, when tribulation and anguish overcome you,
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 then they will call to me, and I will not heed, they will arise in the morning, and not find me.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 For they held hatred for discipline, and they would not accept the fear of the Lord;
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 they would not consent to my counsel, but they detracted from all of my corrections.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Therefore, they shall eat the fruit of their way, and they shall have their fill of their own counsels.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 The loathing of the little ones shall destroy them, and the prosperity of the foolish shall perish them.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 But whoever will listen to me shall rest without terror, and shall have full enjoyment of abundance, without fear of evils.”
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Proverbs 1 >