< Numbers 8 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Speak to Aaron, and you shall say to him: When you place the seven lamps, let the lampstand be set up on the south side. Therefore, give this instruction: that the lamps should look out from the region opposite the north, toward the table of the bread of the presence; they shall give light opposite that area, toward the area that the lampstand faces.”
“Yi magana da Haruna, ka ce masa, ‘Sa’ad da za ka shisshirya fitilun nan bakwai, ka shirya su yadda za su fuskanci gaba domin haskensu yă haskaka ta gaba.’”
3 And Aaron did so, and he placed the lamps on the lampstand, just as the Lord had instructed Moses.
Haka kuwa Haruna ya yi; ya shisshirya fitilun yadda za su fuskanci gaba a kan wurin ajiye fitilan, kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
4 Now this was the workmanship of the lampstand: it was of ductile gold, both the main shaft and all that originated from both sides of the branches. According to the example that the Lord revealed to Moses, so did he make the lampstand.
Ga yadda aka yi wurin ajiye fitilan. An ƙera shi da zinariya daga gindinsa har zuwa sama inda ya buɗu. Aka ƙera wurin ajiye fitilan yadda Ubangiji ya nuna wa Musa.
5 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
6 “Take the Levites from the midst of the sons of Israel, and you shall purify them
“Keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, ka tsarkake su.
7 according to this ritual: Let them be sprinkled with the water of illumination, and let them shave off all the hairs of their body. And when they have washed their garments and have been cleansed,
Ga yadda za ka tsarkake su, ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa; ka sa su aske jikunansu duka su kuma wanke tufafinsu, ta haka za su tsarkake kansu.
8 they shall take an ox from the herd, with its libation of fine wheat flour sprinkled with oil; then you shall receive another ox from the herd for sin.
Ka sa su ɗauki ɗan bijimi tare da lallausan garin hadaya, kwaɓaɓɓe da mai; sa’an nan, kai kuma ka ɗauki ɗan bijimi na biyu na hadaya don zunubi.
9 And you shall bring forward the Levites before the tabernacle of the covenant, calling together all the multitude of the sons of Israel.
Ka kawo Lawiyawa a gaban Tentin Sujada, ka kuma kira taron Isra’ilawa duka.
10 And when the Levites are before the Lord, the sons of Israel shall place their hands upon them.
Za ka kawo Lawiyawa a gaban Ubangiji, Isra’ilawa kuma za su ɗibiya musu hannuwansu.
11 And Aaron shall offer the Levites as a gift in the sight of the Lord, from the sons of Israel, so that they may serve in his ministry.
Haruna zai miƙa Lawiyawa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa daga Isra’ilawa, saboda a shirya su domin aikin Ubangiji.
12 Likewise, the Levites shall place their hands upon the heads of the oxen; you shall make use of one of these for sin, and the other as a holocaust to the Lord, so that you may intercede for them.
“Bayan Lawiyawa sun ɗibiya hannuwansu a kan bijiman, sai ka yi amfani da ɗaya a matsayin hadaya don zunubi ga Ubangiji, ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa, don yin kafara saboda Lawiyawa.
13 And you shall set the Levites in the sight of Aaron and his sons, and you shall consecrate those being offered to the Lord,
Ka kuma sa Lawiyawa su tsaya a gaban Haruna da’ya’yansa, sai ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji.
14 and you shall separate them from the midst of the sons of Israel, so that they may be for me.
Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, Lawiyawa za su zama nawa.
15 And after this, they shall enter the tabernacle of the covenant, in order to serve me. And so shall you purify and consecrate them as an oblation to the Lord. For they were given to me as a gift from the sons of Israel.
“Bayan ka tsarkake Lawiyawa, ka kuma miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, sai su zo su yi aikinsu a Tentin Sujada.
16 I have accepted them in place of the firstborn which open every womb in Israel.
Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra’ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato, dukan’ya’yan farin Isra’ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa.
17 For all the firstborn of the sons of Israel, as much from men as from beasts, are mine. From the day when I struck down all the firstborn in the land of Egypt, I have sanctified them to myself.
Kowane ɗan farin haihuwa, ko mutum, ko dabba a Isra’ila, nawa ne. Sa’ad da na kashe’ya’yan fari a Masar, na keɓe’ya’yan fari na Isra’ilawa wa kaina.
18 And I have taken the Levites in place of all the firstborn of the sons of Israel.
Na kuma ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari maza a Isra’ila.
19 And I have delivered them as a gift to Aaron and his sons, from the midst of the people, in order to serve me, for Israel, in the tabernacle of the covenant, and in order to pray for them, lest there be a scourge among the people, if they were to dare to approach to my Sanctuary.”
Cikin dukan Isra’ilawa, na ba da Lawiyawa kyauta ga Haruna da’ya’yansa, su yi hidima a Tentin Sujada a madadin Isra’ilawa, su kuma yi kafara dominsu saboda kada annoba ta bugi Isra’ilawa sa’ad da suka je kusa da wuri mai tsarki.”
20 And Moses and Aaron, and all the multitude of the sons of Israel, accomplished all that the Lord had commanded Moses concerning the Levites.
Musa, Haruna da kuma dukan taron Isra’ilawa, suka yi da Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
21 And they were purified, and they washed their garments. And Aaron lifted them up in the sight of the Lord, and he prayed for them,
Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma wanke tufafinsu. Sai Haruna ya miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa a gaban Ubangiji, ya kuma yi kafara saboda su don yă tsarkake su.
22 so that, having been purified, they might enter to their duties in the tabernacle of the covenant before Aaron and his sons. Just as the Lord had instructed Moses about the Levites, so was it done.
Bayan haka, sai Lawiyawa suka zo don su yi aikinsu a Tentin Sujada, a ƙarƙashin Haruna da’ya’yansa. Suka yi da Lawiyawa kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
23 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
24 “This is the law of the Levites: From twenty-five years and above, they shall enter to minister in the tabernacle of the covenant.
“Wannan ya shafi Lawiyawa ne, wato, mazan da suka kai shekara ashirin da biyar, ko fiye, za su zo su yi aiki a Tentin Sujada,
25 And when they will have completed the fiftieth year of age, they shall cease to serve.
amma in suka kai shekaru hamsin da haihuwa, dole su huta daga wannan aiki na yau da kullum, su kuma daina aiki.
26 And they shall be the ministers of their brothers in the tabernacle of the covenant, in order to care for the things that have been commended to them, but not to perform the works themselves. So shall you assign the Levites in their duties.”
Za su iya taimakon’yan’uwansu cikin tafiyar da ayyuka a Tentin Sujada, amma su kansu ba za su yi aikin ba. Haka fa za ka ba wa Lawiyawa aikinsu.”

< Numbers 8 >