< Numbers 4 >

1 And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 “Take a total of the sons of Kohath from the midst of the Levites, by their houses and families,
“Ku yi ƙidaya Kohatawa daga Lawiyawa, bisa ga kabilarsu da iyalansu.
3 from thirty years and above, even to the fiftieth year, of all who enter so as to stand and minister in the tabernacle of the covenant.
Ku ƙidaya dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin da suka zo domin aiki a Tentin Sujada.
4 This is the service of the sons of Kohath: the tabernacle of the covenant and the Holy of holies.
“Ga aikin Kohatawa a Tentin Sujada, kulawa da kayayyaki mafi tsarki.
5 Aaron and his sons shall enter, when the camp is going to move, and they shall take down the veil, which hangs before the entrance, and they shall wrap the ark of the testimony in it,
Lokacin da za a tashi daga sansani, Haruna da’ya’yansa za su shiga ciki su kunce labulen kāriya, su rufe Akwatin Alkawari da shi.
6 and they shall cover it further with a veil of violet skins, and they shall extend over it a cloth made entirely of hyacinth, and they shall draw in the bars.
Sa’an nan su rufe shi da fatun shanun teku, su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi a bisansa, su sa masa sandunansa.
7 Likewise, they shall wrap the table of the presence in a cloth of hyacinth, and they shall place with it the censers and little mortars, the cups and bowls for pouring out libations; the bread shall be always on it.
“A bisa teburin Burodin Ajiyewa, za su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi, a kansa kuma su sa farantai, kwanoni da manyan kwanoni, da tuluna don hadayun sha; da burodin da zai ci gaba da kasancewa a kansa.
8 And they shall extend over it a cloth of scarlet, which they shall further cover with a veil of violet skins, and they shall draw in the bars.
A bisa waɗannan za su shimfiɗa jan zane, su rufe su da fatun shanun teku, su kuma zura masa sandunansa.
9 They shall take also a cloth of hyacinth, with which they shall cover the lampstand with the lamps, and its tongs, and the candle snuffers, and all the vessels of oil, which are necessary for the preparation of the lamps.
“Za su ɗauki zane mai ruwan shuɗi su rufe wurin ajiye fitilan da yake don fitilu, tare da fitilunsa, lagwaninsa da farantansa, da dukan tulunansa don man amfaninsu.
10 And over all this they shall place a covering of violet skins, and they shall draw in the bars.
Sa’an nan su naɗe shi da kuma dukan kayayyakinsa a cikin fatar shanun teku, su sa shi a kan sandan ɗaukarsa.
11 And certainly they shall wrap the golden altar in a hyacinth garment, and they shall extend over it a covering of violet skins, and they shall draw in the bars.
“A kan bagaden zinariya, za su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi, su kuma rufe shi da fatar shanun teku, sai a zura masa sandunansa.
12 All the vessels with which they minister in the Sanctuary they shall wrap in a cloth of hyacinth, and they shall extend over it a covering of violet skins, and they shall draw in the bars.
“Za su ɗauki dukan kayayyakin da ake amfani da su a wuri mai tsarki, su nannaɗe su da zane mai ruwan shuɗi, su rufe shi da fatar shanun teku, sa’an nan a sa su a kan sandan ɗaukarsa.
13 Moreover, they shall cleanse the altar of ashes, and they shall wrap it in a purple garment,
“Za su kwashe tokar da take a bagaden tagulla, su shimfiɗa zane mai ruwan shuɗi a bisansa.
14 and they shall place it with all the vessels which they use in its ministry, that is, receptacles for fire, small hooks as well as forks, larger hooks and shovels. They shall cover all the vessels of the altar together with a veil of violet skins, and they shall draw in the bars.
Sa’an nan su sa a kansa dukan kayayyakin da aka yi amfani da su a bagaden, haɗe da farantai don wuta, cokula masu yatsu don nama, manyan cokula, da darunan yayyafawa. A kansa za su shimfiɗa murfi na fatun shanun teku, su zura sandunan ɗaukarsa.
15 And when Aaron and his sons have wrapped the Sanctuary and its vessels at the dismantling of the camp, then the sons of Kohath shall enter, so as to carry what has been wrapped. And they shall not touch the vessels of the Sanctuary, lest they die. These are the burdens of the sons of Kohath concerning the tabernacle of the covenant.
“Bayan Haruna da’ya’yansa suka gama rufe kayayyaki masu tsarki da dukan abubuwa masu tsarki, sa’ad da kuma aka shirya tashi daga sansani, sai Kohatawa su zo gaba, su ɗauka. Amma kada su taɓa abubuwa masu tsarki, don kada su mutu. Kohatawa za su ɗauki abubuwan da suke cikin Tentin Sujada.
16 Over them shall be Eleazar, the son of Aaron the priest, to whom belongs the care of the oil to prepare the lamps, and the incense compound, and the sacrifice, which is offered continually, and the oil of unction, and whatever pertains to the service of the tabernacle, and all the vessels that are in the Sanctuary.”
“Eleyazar ɗan Haruna firist zai lura da man fitila da turare da hadaya ta gari na kullum da kuma keɓaɓɓen mai. Shi ne zai lura da dukan tabanakul da duk abin da yake cikinsa da kuma kayayyaki da abubuwan masu tsarki.”
17 And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
18 “Do not be willing to lose the people of Kohath from the midst of the Levites.
“Ku tabbata cewa ba a kawar da zuriyar Kohatawa daga Lawiyawa ba.
19 But do this for them, so that they may live, and so that they may not die by touching the Holies of holies. Aaron and his sons shall enter, and they shall assign the work of each one, and they shall determine what each one ought to carry.
Saboda su rayu, kada su mutu sa’ad da suka zo kusa da abubuwa mafi tsarki, a yi musu wannan, wato, Haruna da’ya’yansa za su shiga wuri mai tsarki su ba wa kowane mutum aikinsa da kuma abin da zai ɗauka.
20 Let no others, out of curiosity, see the things that are in the Sanctuary before they are wrapped, otherwise they shall die.”
Amma kada Kohatawa su shiga don su dubi abubuwa masu tsarki, ko na ɗan ƙanƙanin lokaci, in ba haka ba za su mutu.”
21 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
22 “Now also take a total of the sons of Gershon, by their houses and families and kinships,
“Ka ƙidaya mutanen Gershon bisa ga iyalansu da kabilarsu.
23 from thirty years and above, even to fifty years. Number all those who enter and minister in the tabernacle of the covenant.
Ka ƙidaya maza masu shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada.
24 This is the duty of the family of the Gershonites:
“Ga aikin kabilar Gershonawa yayinda suke aiki, suke kuma ɗaukar kaya.
25 to carry the curtains of the tabernacle, and the roof of the covenant, the other covering, and the veil over everything, and the violet tent, which hangs at the entrance of the tabernacle of the covenant,
Za su ɗauki labulen tabanakul, Tentin Sujada, kayan da za a rufe shi, da kuma kayan da za a rufe shi daga waje na fatun rufuwa na shanun teku, labulen ƙofar Tentin Sujada,
26 the curtains of the atrium, and the veil at the entrance, which is before tabernacle. Everything that pertains to the altar, the cords, and the vessels of the ministry
labulen filin da yake kewaye da tabanakul da bagade, labulen ƙofa, igiyoyi da kuma dukan abubuwan da ake amfani da su wajen hidima. Geshonawa za su yi dukan abin da ya kamata a yi da waɗannan abubuwa.
27 the sons of Gershon shall carry, under the orders of Aaron and his sons. And so shall each one know to which burden he ought to surrender.
Dukan hidimominsu, ko na ɗauko, ko kuma na yin wani aiki, za a yi su ne bisa ga umarnin Haruna da’ya’yansa. Za ka ba su dukan kayan da za su ɗauka a matsayin hakkinsu.
28 This is the service of the family of the Gershonites, in the tabernacle of the covenant, and they shall be under the hand of Ithamar, the son of Aaron the priest.
Wannan shi ne hidimar da kabilar Gershonawa za su yi a Tentin Sujada. Ayyukansu za su kasance bisa ga umarnin Itamar ɗan Haruna firist.
29 Likewise, you shall take a census of the sons of Merari, by the families and houses of their fathers,
“Ka ƙidaya kabilar Merari bisa ga kabilarsu da iyalansu.
30 from thirty years and above, even to fifty years, of all who enter to the office of their ministry and to the service of the covenant of the testimony.
Ka ƙidaya maza daga masu shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada.
31 These are their burdens: They shall carry the panels of the tabernacle and its bars, the columns and their bases,
Ga aikinsu sa’ad da suke hidima a Tentin Sujada, za su ɗauki katakan tabanakul, sandunansa da dogayen sandunansa, da rammukansa,
32 also the columns surrounding the atrium, with their bases and tent pegs and cords. They shall accept by number all the vessels and articles, and so shall they carry them.
har ma da dogayen sandunan kewayen filin da rammukansu, turakun tenti, igiyoyi, da dukan kayayyaki, da kuma dukan abubuwan da suke dangane da amfaninsu. Ka ba wa kowane mutum ayyuka na musamman da zai yi.
33 This is the office of the family of the Merarites, and their ministry for the tabernacle of the covenant. And they shall be under the hand of Ithamar, the son of Aaron the priest.”
Wannan ce hidimar da mutanen Merari za su yi a aikin Tentin Sujada, a ƙarƙashin jagorancin Itamar ɗan Haruna, firist.”
34 Therefore, Moses and Aaron, and the leaders of the assembly, took a census of the sons of Kohath, by the kinships and houses of their fathers,
Musa, Haruna da kuma shugabannin jama’a, suka ƙidaya Kohatawa ta kabilarsu da kuma iyalansu.
35 from thirty years and above, even to the fiftieth year, of all who enter to the ministry of the tabernacle of the covenant.
Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada,
36 And there were found two thousand seven hundred fifty.
da aka ƙidaya, kabila-kabila, su 2,750 ne.
37 This is the number of the people of Kohath, who enter the tabernacle of the covenant. These Moses and Aaron numbered according to the word of the Lord by the hand of Moses.
Jimillar dukan waɗanda suke na kabilan Kohatawa, waɗanda suka yi hidimar aiki a Tentin Sujada ke nan. Musa da Haruna sun ƙidaya su bisa ga umarnin Ubangiji.
38 The sons of Gershon also were numbered by the kinships and houses of their fathers,
Aka ƙidaya mazan Gershonawa ta kabilansu da kuma iyalansu.
39 from thirty years and above, even to the fiftieth year, all who enter so as to minister in the tabernacle of the covenant.
Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada,
40 And there were found two thousand six hundred thirty.
da aka ƙidaya kabila-kabila da kuma iyali-iyali, su 2,630 ne.
41 This is the people of the Gershonites, whom Moses and Aaron numbered according to the word of the Lord.
Jimillar waɗanda suke na kabilar Gershonawa ke nan, waɗanda suka yi hidimar aiki a Tentin Sujada. Musa da Haruna sun ƙidaya su bisa ga umarnin Ubangiji.
42 The sons of Merari also were numbered by the kinships and houses of their fathers,
Aka ƙidaya mazan Merari ta kabilarsu da kuma iyalansu.
43 from thirty years and above, even to the fiftieth year, all who enter to fulfill the rituals of the tabernacle of the covenant.
Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki a Tentin Sujada,
44 And there were found three thousand two hundred.
da aka ƙidaya kabila-kabila, su 3,200 ne.
45 This is the number of the sons of Merari, whom Moses and Aaron counted according to the command of the Lord by the hand of Moses.
Jimillar waɗanda suke na kabilar Merari ke nan. Musa da Haruna suka ƙidaya su bisa ga umarnin Ubangiji.
46 All who were counted from the Levites, and whom, by name, Moses and Aaron, and the leaders of Israel, counted by the kinships and houses of their fathers,
Saboda haka, Musa, Haruna da shugabannin Isra’ila, suka ƙidaya dukan Lawiyawa kabila-kabila da kuma iyali-iyali.
47 from thirty years and above, until the fiftieth year, entering for the ministry of the tabernacle and carrying the burdens,
Dukan maza daga shekara talatin zuwa hamsin waɗanda sukan zo hidimar aiki da kuma ɗaukar Tentin Sujada
48 were together eight thousand five hundred eighty.
jimillarsu ta kai 8,580.
49 Moses took a census of them, according to the word of the Lord, each one according to their office and their burdens, just as the Lord had instructed him.
Bisa ga umarnin Ubangiji ta wurin Musa, aka ba kowa aikinsa, aka kuma faɗa musu abin da za su ɗauka. Ta haka aka ƙidaya su, yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 4 >